< Job 9 >

1 Darauf gab Job zur Antwort:
Sai Ayuba ya amsa,
2 "Wahrhaft, ich weiß, daß es so ist. Wie könnte gegen Gott ein Mensch obsiegen?
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 Hat einer Lust, mit ihm zu streiten, gibt er auf tausend nicht ein Wort zu hören.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 Ist einer noch so klug und stark, wer trotzte ihm und bliebe heil?
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 Der Berge so versetzt, daß man nicht merkt, daß er im Zorn sie umgestürzt,
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 der zittern macht der Erde Bau, daß ihre Säulen wanken,
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 der nicht mehr scheinen heißt die Sonne, und Sterne unter Siegel legt,
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 der ganz allein den Himmel spannte, auf Wolken schreitet,
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 den Bären und Orion schuf, den Siebenstern, des Südens Kreuz,
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 der groß und unerforschlich waltet und Wunder wirket ohne Zahl:
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 Er macht sich an mich her, bevor ich's sehe, dringt auf mich ein, eh ich's bemerke.
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 Und packt er zu, wer hält ihn ab? Wer sagt zu ihm: 'Was tust du da?'
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 Wenn seinem Zorne Gott nicht wehrt, dann winden sich zu seinen Füßen selbst des Ungestüms Gehilfen.
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 Wie kann dann ich ihm Rede stehen, ihm gegenüber meine Worte wählen,
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 ich, der ich nicht Bescheid darf geben, mag ich im Recht auch sein, nein, meinen Richter noch anwinseln muß?
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 Wenn ich ihn riefe, gäbe er mir Antwort? Ich glaub' es nicht, daß er auf meine Stimme hörte,
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 er, der mich für ein Härchen packt, mir grundlos viele Wunden schlägt.
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 Er läßt mich nicht zu Atem kommen, weil er mit Bitterkeit mich sättigt.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 Wenn's auf die Kraft ankommt, dann ist er stark, und gilt es zu beweisen, wer zeugt für mich?
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 Bin ich im Recht, dann zeiht mich doch sein Mund des Unrechts, bin ich unschuldig, stellt er mich doch als schuldig hin.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 Und wüßte ich nicht selber, daß ich schuldlos bin, wegwürfe ich mein Leben.
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 Nun ist es so; drum sage ich es offen. Er bringt den Frommen gleich dem Frevler um.
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 Die Geißel tötet blindlings; er lacht ob der Unschuldigen Verzweiflung.
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 Die Welt ist somit ausgeliefert in eines Ungerechten Hand, der seinen Strafgerichten das Gesicht verhüllt. Ist's dem nicht so, wie ist es dann?
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 Und meine Zeit läuft schneller als ein Läufer; sie flieht und sieht das Glück nicht mehr,
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 so flüchtig wie die Binsenschiffe, rasch wie der beutegierige Aar.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 Nie kann ich sagen: 'Ich will mein Leid vergessen, mein Trauern lassen, heiter sein.'
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 Mir graut vor allen meinen Schmerzen; ich weiß: Du sprichst mich nimmer los.
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 Ich soll nun einmal schuldig sein. Wozu mich zwecklos mühen?
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 Und wüsche ich mich weiß wie Schnee und reinigte mit Lauge mir die Hände,
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 dann tauchtest Du mich um so tiefer in den Kot, daß meine Kleider selbst vor mir sich ekelten.
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 Er ist kein Mensch wie ich, dem ich erwiderte: 'Gehn wir zusammen vor Gericht!'
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 Wenn einen Schiedsmann zwischen uns es gäbe, der beide unter seine Aufsicht stellte,
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 der seinen Stock von mir fernhielte; daß mich die Angst vor jenem nicht betäubte,
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 dann wollt' ich furchtlos frei aussprechen, daß er - ich weiß es - gegen mich nicht ehrlich ist."
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.

< Job 9 >