< Job 4 >

1 Da gab ihm Eliphaz aus Teman also Antwort:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 "Hat man vor dich zur Prüfung je ein Ding gebracht, worüber du den Mut verloren hättest? Wer konnte je den Worten Einhalt tun?
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3 Fürwahr, so viele hast du selbst belehrt, so manchen schwachen Arm gestählt.
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4 Den Strauchelnden hielt aufrecht deine Rede; die müden Kniee stärktest du.
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 Jetzt kommt's an dich, da wirst du mutlos; wo dich's erfaßt, verzweifelst du.
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 War deine Gottesfurcht nicht dein Vertrauen, und dein unsträflich Leben deine Hoffnung?
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
7 Bedenke nur: Wer kommt je schuldlos um? Wo gehen Redliche zugrunde?
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 Die Unrecht pflügen, Böses säen, die ernten's auch. So weiß ich es.
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 Durch Gottes Odem gehen sie zugrunde; durch seinen Zornhauch sterben sie.
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10 Der Löwen Stimmen selber, das Gebrüll der Leuen, der jungen Löwen Zähne werden ausgetilgt.
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11 Der Löwe geht zugrunde aus Beutemangel; der Löwin Junge müssen sich zerstreuen.
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
12 Zu mir drang ein verstohlen Wort; mein Ohr vernahm davon nur ein Geflüster.
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13 Im Wundertraum, bei Nachtgesichten, wenn Tiefschlaf auf die Menschen fällt,
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14 da fuhr in mich ein Schrecken und ein Zittern, und Angst ließ mein Gebein erbeben.
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15 Und über meinen Rücken lief es kalt; ein Schauder schüttelt' meinen Leib.
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 Das Unbekannte stand vor mir; vor meinem Auge schwebte her ein Schatten. - Ein Säuseln hörte ich und eine Stimme:
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 'Ist gegen Gott ein Mensch gerecht; vor seinem Schöpfer einer rein?'
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 Er traut dies seinen Dienern selbst nicht zu, und seinen Engeln flößt er Schrecken ein.
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 Nun vollends gar der Lehmhausmensch, der Sterbliche, aus Staub gebaut, noch leichter als die Motten zu zerdrücken!
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
20 Vom Morgen bis zum Abend werden sie vernichtet; unwiderruflich gehen sie zugrunde.
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
21 Ja, wird denn nicht ihr Vorzug ihnen weggenommen? Durch Unvernunft nur sterben sie."
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’

< Job 4 >