< Job 30 >
1 "Und jetzt verlachen solche mich, die jünger sind als ich, ja solche, deren Väter ich nicht beigesellen möchte meinen Herdenhunden!
“Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
2 Was sollte mir selbst ihrer Hände Kraft, denn Rüstigkeit geht ihnen doch verloren!
Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
3 Durch Mangel und durch harten Hunger sollen sie sich Nahrung aus der Wüste holen, dem Lande des Orkans und Sturmes.
Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
4 Sie sollten Melde pflücken am Gesträuche, und ihre Nahrung seien Ginsterwurzeln!
A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
5 Von Wasserstellen sollten sie vertrieben werden! Man schreie über sie wie Diebe,
An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
6 daß sie in schauerlichen Schluchten, in Erdlöchern und Felsenhöhlen siedeln,
An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
7 und daß sie im Gebüsche gröhlen und unter Nesseln sich zusammenkauern!
Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
8 Sie, eine Brut so schlecht und ehrlos, sie sollten tief im Staube liegen!
Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
9 Und jetzt bin ich ihr Spottgesang; ich diene ihnen zum Gerede.
“Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
10 Ja, sie verabscheun mich und rücken fern von mir und scheun sich nicht, mir ins Gesicht zu speien.
Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
11 Er löste mir das Diadem und warf mich auf den Boden, daß sie den Zügel vor mir schießen lassen konnten.
Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
12 Zur Prüfung stehn die Gegner auf; sie lähmen mir die Füße und werfen gegen mich die Wege für ihr Unheil auf.
A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
13 Sie reißen meine Pfade auf, verhelfen mir zum Falle, und niemand hindert sie.
Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
14 Sie kommen wie ein breiter Dammbruch her; sie wälzen sich mit Ungestüm heran.
Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
15 Da kommen Schrecken über mich; dem Wind gleich jagt mein Glück davon; fort zieht mein Heil wie eine Wolke.
Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
16 Mein Leben ist in mir zerflossen, und jammervolle Tage halten mich gefesselt.
“Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
17 Des Nachts bohrt's mir in dem Gebein; auf meinen bloßgelegten Knochen kann ich nimmer liegen.
Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
18 Mit Allgewalt packt er mich an und schnürt mich in des Unterkleides Schlitze ein.
A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
19 Er wirft mich in den Schmutz; dem Staub, der Asche bin ich gleich. -
Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
20 Ich schreie auf zu Dir. Doch Du hörst nicht auf mich. Ich halte ein; da gibst Du auf mich acht.
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
21 Du zeigst Dich grausam gegen mich und geißelst mich mit Deiner starken Hand.
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
22 Du schickst den Wind, mich zu entführen; der Sturm fährt mit mir auf und ab.
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
23 Ich weiß ja wohl: Du willst zum Tod mich treiben, in das Versammlungshaus für alles Lebende.
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
24 Auf Wunsch jedoch greift er nicht zu, schreit man in seinem Unglück drob um Hilfe. -
“Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
25 Beweinte ich nicht den Unseligen; war nicht mein Herz des Armen wegen sehr betrübt? -
Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
26 Weil ich auf Glück gehofft, doch Unheil kam; auf Licht geharrt, doch Dunkel kam,
Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
27 so ist im Aufruhr ohne Unterlaß mein Inneres. Des Leidens Tage überfielen mich.
Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
28 Tieftraurig wandle ich einher, wo keine Sonne scheint. Ich trete dem Vereine bei, wo ich nur heulen kann.
Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
29 Der Schakale Vereinsbruder bin ich und ein Gesell dem Vogel Strauß.
Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
30 Zu schwarz ward meine Haut, daß sie mir bliebe, und mein Gebein ist mir von Glut verbrannt.
Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
31 So diente meine Harfe mir zum Trauerliede, zu bitterem Schluchzen die Schalmei."
Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.