< Job 21 >
1 Darauf erwidert Job und spricht:
Sai Ayuba ya amsa,
2 "Mögt ihr auf meine Rede nochmals hören, und wär's zu eurem Zeitvertreib!
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Ertragt mich! Laßt mich, reden! Dann scheltet nur, wenn ich geredet!
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 Erhebe ich denn gegen einen Menschen Klage? Oder - warum soll ich nicht ungeduldig werden dürfen?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Zu mir kehrt euch, erstarret! Die Hand legt auf den Mund!
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Ich werde ganz erschüttert, denke ich daran; an Leib und Seele zittere ich.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Wie kommt's, daß Frevler leben dürfen und alternd noch an Kräften wachsen?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Bei ihnen bleibt ihr Stamm, und er gedeiht, solang sie leben, und stets vor Augen bleiben ihnen ihre Sprößlinge.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Und sicher vor Gefahr sind ihre Häuser; die Gottesrute trifft sie nicht.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Sein Stier bespringt und läßt es nicht entgleiten, und seine Kuh kalbt leicht und tut nicht eine Fehlgeburt.-
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 Gleich einer Herde lassen sie die Kinderschar hinaus, und munter hüpfen ihre Jungen.
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 Sie spielen froh zu Pauken und zu Zithern und freuen sich beim Flötenschalle.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 Ihr Leben geht im Glück zu Ende; sie steigen zu der Unterwelt in Frieden (Sheol )
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol )
14 und sagen doch zu Gott: 'Du bleib uns fern!' 'Wir wollen nichts von Deinen Wegen wissen!'
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 'Was soll es, daß wir dem Allmächtigen dienen? Was nützt es uns, ihn bittend anzugehen?'
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 Nun, läge nicht ihr Glück in ihrer Hand, dann wäre mir das Planen dieser Frevler unbegreiflich.
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 Wie oft erlischt der Frevler Leuchte und überfällt sie ihr Verderben? Wie oft teilt er in seinem Zorne Schmerzen aus? -
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 Sie sollen werden wie das Stroh vorm Winde, wie Spreu, vom Sturm entführt!
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 'Gott hat sein Unheil eben dessen Kindern aufgespart.' Er zahle ihm es heim, daß er es selber fühle!
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 Er selber sollte seinen Becher kosten und von dem Grimm des Höchsten trinken müssen!
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 Was braucht ihn denn zu kümmern, wie's seinem Haus nach seinem Tode geht, wenn seiner Monde Zahl zu Ende ist?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Kann man denn Gott das Wissen lehren, da er doch von der Höhe aus verfügt?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 Der eine stirbt in vollem Glücke, ganz ruhig, wohlgemut.
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 Von Fett sind seine Lenden voll; sein Körper wird mit Mark getränkt.
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 Der andre stirbt verzweiflungsvoll, hat niemals von dem Glück gekostet.
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 Zusammen liegen sie im Staube; Gewürm deckt beide zu.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Ich kenne eure Meinung wohl; ihr ziehet an den Haaren Gründe gegen mich herbei.
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 Ihr sagt: 'In welcher Lage ist das Haus des edlen Mannes?' 'In welcher ist das Wohngezelt der Frevler?'
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 Befragt ihr nicht die Leute, die auf den Lauf der Welten achten? Und ihre Zeugnisse könnt ihr nicht ablehnen.
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 Der Frevler bleibt vom Unheilstag verschont, vom Tag, wo Steuern eingetrieben werden.
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Wer hält ihm seinen Wandel vor, und wer vergilt ihm, was er tat?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 Er wird zu Grab getragen, und auf dem Grabespolster ruht er ungestört.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 Des Grabes Schollen sind ihm süß. So lockt er alle Welt sich nach, und vor ihm schreiten Zahllose einher.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Wie leer ist euer Trost! Und eure Antworten sind unaufrichtig."
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”