< Job 12 >

1 Darauf gab Job zur Antwort:
Sai Ayuba ya amsa,
2 "Wahrhaftig, ihr seid Leute; ausstirbt mit euch die Weisheit.
“Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
3 Ich habe aber auch Verstand wie euer einer, ich falle gegen euch nicht ab. Wem wären solche Dinge fremd? -
Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
4 Dem Nächsten diene ich zum Schimpf, dem, der zu Gott ruft und den er erhört, dem vollkommenen Gerechten, zum Gespött.
“Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
5 Ich gleiche einer Nessel, gar verachtenswert, nach Ansicht Glücklicher für Fußtritte ausersehen.
Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
6 Den Räubern aber sind die Zelte sicher, und Sicherheit genießen, die Gott reizen für das, was Gott in ihreHände hat gegeben.
Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
7 Befrage nur die Tiere! Sie können es dir sagen; die Vögel auch beweisen dir's.
“Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
8 Schau dir die Erde an! Sie lehrt es dich; die Fische in dem Meer bezeugen dir's:
Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
9 Wer nur in aller Welt weiß nicht, daß Gottes Hand dies hat geschaffen,
Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
10 daß jedes Wesen ist in seiner Hand, der Odem aller Sterblichen? -
Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
11 Ist nicht das Ohr zum Worteprüfen so geschaffen, gerade wie der Gaumen, daß er Speise koste? -
Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
12 Ist Weisheit bei den Alten, Verstand bei langem Leben bloß zu finden,
Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
13 dann muß bei ihm recht große Weisheit, Verstand und kluger Rat zu finden sein.
“Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
14 Was er zerstört, das baut man nimmer auf, und nimmt er jemanden gefangen, der wird nicht wieder frei.
Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
15 Wenn er den Wassern wehrt, dann bleiben sie an Ort und Stelle; wenn er sie ledig läßt, aufwühlen sie die Erde.
Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
16 Von ihm kommt Stärke und Erfolg; sein ist der Irrende, sein der Verführer.
Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
17 Er, der da Räte barfuß ziehen läßt und Richtern den Verstand wegnimmt,
Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
18 der Königen die Diademe löst und ihnen Stricke um die Hüften legt,
Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
19 der Priester barfuß ziehen läßt und der Beamte stürzt,
Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
20 der stocken macht geübte Redner und Greisen den Verstand wegnimmt,
Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
21 der Schande ausgießt über Vornehme und Höflingen die Schärpen lockert,
Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
22 der Tiefes aus dem Dunkel zieht und an das Licht das Finstere bringt,
Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
23 der Heiden in die Irre führt und sie vernichtet und Heidenvölker niederstreckt und liegen läßt,
yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
24 der zagen macht die Landeshäupter und sie in auswegloser Wirrnis irreführt,
Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
25 daß sie in finsterem Dunkel tappen und der sie wie Betrunkene taumeln macht."
Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.

< Job 12 >