< 5 Mose 33 >

1 Dies ist der Segen, mit dem Moses, der Mann Gottes, die Söhne Israels vor seinem Tode gesegnet hat.
Wannan ita ce albarkar da Musa mutumin Allah ya furta a kan Isra’ilawa, kafin yă rasu.
2 Er sprach: "Vom Sinai kam her der Herr, erstrahlte ihnen von Seïr. Er glänzte auf von Pharans Bergen und kam von Kades' Randgebieten, des Haderwassers Randgebirge.
Ya ce, “Ubangiji ya zo daga Sinai ya haskaka a bisansu daga Seyir; ya haskaka daga Dutsen Faran. Ya zo tare da dubban tsarkakansa daga kudu, daga gangara dutsensa.
3 Ja, Freund des Volkes! Bei dir sind alle seine heiligen Geheimnisse; sie sind dir anvertraut; man lernt von deinen Weisungen.
Tabbatacce kai ne wanda yake ƙaunar mutane; dukan tsarkaka suna a hannunka. A ƙafafunka, duk suka rusuna, daga wurinka kuma suka karɓi umarni,
4 Die Lehre hat uns Moses übergeben zum Erbe der Gemeinde Jakobs.
dokar Musa ta ba mu dokoki, mallakar taron Yaƙub.
5 Ein König wurde er in Jeschurun, als sich des Volkes Häupter sammelten, in eins die Stämme Israels.
Shi ne sarki a bisa Yeshurun sa’ad da shugabannin mutane suka taru, tare da kabilan Isra’ila.
6 Es lebe Ruhen, sterbe nimmer aus! Doch seine Wichte seien gezählt!"
“Bari Ruben yă rayu, kada yă mutu, kada mutanensa su zama kaɗan.”
7 Dies sprach er über Juda: "Auf Judas Stimme höre, Herr! Zu seinem Volke bringe ihn! Kampfscharen hat er eine Menge, und Du bist Hilfe wider seine Dränger."
Ya kuma faɗa wannan game da Yahuda, “Ka ji, ya Ubangiji, kukan Yahuda; ka kawo shi wurin mutanensa. Da hannuwansa ya kāre kansa. Ka taimake shi a kan maƙiyansa!”
8 Über Levi sprach er: "Der Dir geweihte Mann hat Deine heiligen Lose, er, den Du einst zu Massa prüftest, auszanktest an dem Haderwasser.
Game da Lawi ya ce, “Tummim da Urim na mutumin da ka nuna masa tagomashi ne. Ka gwada shi a Massa; ka yi faɗa da shi a ruwan Meriba.
9 Er aber sprach von Vater und von Mutter: 'Ich kenne diese nicht', der seine Brüder nicht mehr ansah und seine Kinder nicht mehr kannte. Sie hielten sich an Dein Gebot und wahrten Deinen Bund.
Ya yi zancen mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, ‘Ban kula da su ba.’ Bai gane da’yan’uwansa ba, ko yă yarda da’ya’yansa, amma ya kiyaye maganarka ya tsare alkawarinka.
10 Sie lehrten Jakob Deine Rechte und Deine Lehre Israel. Sie legen Rauchwerk vor Dein Angesicht, auf Deinen Altar Ganzopfer.
Ya koyar da farillanka ga Yaƙub, dokarka kuma ga Isra’ila. Ya miƙa turare a gabanka da kuma hadaya ta ƙonawa ɗungum a kan bagadenka.
11 Herr! Segne seinen Wohlstand! Laß seiner Hände Tun Dir wohlgefallen! Zerschmettere die Lenden seiner Gegner, daß seine Hasser nimmer sich erheben!"
Ka albarkaci ɗaukan dabarunsa, ya Ubangiji, ka kuma ji daɗin aikin hannuwansa. Ka murƙushe kwankwaso waɗanda suka tayar masa; ka bugi abokan gābansa har sai ba su ƙara tashi ba.”
12 Über Benjamin sprach er: "In Ruhe wohnt durch ihn des Herren Liebling; er schützt ihn allezeit, wohnt er doch zwischen seinen Schultern! -
Game da Benyamin ya ce, “Bari ƙaunataccen Ubangiji yă zauna lafiya kusa da shi, gama yana tsare shi dukan yini, wanda kuma Ubangiji yake ƙauna yana zama a tsakanin kafaɗunsa.”
13 Über Joseph sprach er: "Sein Land sei von dem Herrn gesegnet! das Köstlichste vom Himmel droben und drunten von der Wasserflut sei ihm zuteil!
Game da Yusuf ya ce, “Bari Ubangiji yă albarkaci ƙasarsa da raɓa mai daraja daga sama a bisa da kuma zurfin ruwan da suke kwance a ƙarƙashi;
14 Das Köstlichste, was je die Sonne lockt und was die Monde sprossen lassen,
da abubuwa masu kyau da rana take kawo, da kuma abubuwa mafi kyau da wata zai iya haifar;
15 das Beste, was die Ahnen hatten, das Köstlichste der alten Hirten,
da zaɓaɓɓun kyautai na daɗaɗɗun duwatsu, da kyawawan amfani na madawwaman tuddai.
16 das Köstlichste des Bodens, seiner Fülle: die Gnade dessen, der im Dornbusch wohnt, es komme auf das Haupt des Joseph, auf des Geweihten Scheitel unter seinen Brüdern!
Tare da kyautai mafi kyau na duniya da cikarta, da tagomashi na wanda yake zama a ƙaramin itace mai ƙonewa. Bari duk waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin sarki a cikin’yan’uwansa.
17 Sein Erstgeborner, stiergleich, habe Hoheit, und Wildstierhörner seien seine Hörner! Mit ihnen stoße er die Völker nieder bis zu der Erde Enden allzumal! Das sind des Ephraim Zehntausende und des Manasse Tausende."
Cikin daraja yana yi kamar ɗan fari na bijimi; ƙahoninsa ƙahonin ɓauna ne. Tare da su zai tukwiyi al’ummai, har ma da waɗanda suke ƙarshen duniya. Haka dubu dubban Efraim suke; haka dubban Manasse suke.”
18 Über Zabulon sprach er: "Erfreue dich an deinen Fahrten, Zabulon, und deinen Zelten, Issakar!
Game da Zebulun ya ce, “Ka yi farin ciki, Zebulun, a fitowarka, kai kuma Issakar, a cikin tentunanka.
19 Mit Völkern in dem Bergland stoßen sie zusammen; sie opfern Siegesopfer dort. Sie schleppen fort der Meere Schätze und fremder Küsten Abgaben."
Za su kira mutane zuwa dutse, a can za su miƙa hadayun adalci; za su yi biki a yalwan tekuna, a dukiyoyin da aka ɓoye a cikin yashi.”
20 Über Gad sprach er: "Gepriesen ist der herdenreiche Gad. Er lagert wie ein Löwe, zerschmettert Speer und Schild und Helm.
Game da Gad ya ce, “Mai albarka ne wanda ya fadada mazaunin Gad! Gad yana zama a can kamar zaki, yana yayyage a hannu da kai.
21 Und er ersah sich einen Edelsitz; denn er zerteilte eines Feindesfürsten Land. Des Volkes Häupter feuerte er an und tat mit Israel, was recht dem Herrn und billig war." -
Ya zaɓi ƙasa mafi kyau wa kansa; aka ajiye masa rabon shugaba. Sa’ad da shugabannin mutane suka taru, ya aikata adalcin Ubangiji da kuma hukuncinsa game da Isra’ila.”
22 Und über Dan sprach er: "Dan ist ein Löwenjunges, das sich aus Basan gut versorgt."
Game da Dan ya ce, “Dan ɗan zaki ne, yana tsalle daga Bashan.”
23 Und über Naphtali sprach er: "Zufrieden satt ist Naphtali, des Herren Segens voll, wenn er See und Südland sich zu eigen nimmt."
Game da Naftali ya ce, “Naftali ƙosasshe ne da tagomashin Ubangiji, ya kuma cika albarkarsa; zai gāji gefen kudu zuwa tafki.”
24 Und über Asser sprach er: "Der Söhne meistgesegneter sei Asser! Er sei der Liebling seiner Brüder! Er bade seinen Fuß in Öl! -
Game da Asher ya ce, “Mafi albarka na’ya’yan, shi ne Asher; bari yă sami tagomashi daga’yan’uwansa, bari kuma yă wanke ƙafafunsa a cikin mai.
25 Dein Schutz ist Erz und Eisen, und deine Waffen sind dein Stolz.
Madogaran ƙofofinka za su zama ƙarfe da tagulla, ƙarfinka kuma zai zama daidai da kwanakinka.
26 Wie Jeschuruns Gott, gibt es keinen. Er fuhr am Himmel hin in seiner Hoheit in den Wolken, als deine Hilfe.
“Babu wani kamar Allah na Yeshurun, wanda yake hawa a bisa sammai don yă taimake ka a kan gizagizai kuma a cikin darajarsa.
27 Bis jetzt war Gott voll Liebe, gütig gegen seine Treuen. Er hat den Feind vor dir verjagt und hat gesagt: Vertilge!
Allah madawwami shi ne mafakarka, a ƙarƙashina kuma madawwamin hannuwa ne. Zai kore abokin gābanka a gabanka, yana cewa, ‘Ka hallaka shi!’
28 Er läßt im Sichern wohnen Israel, unnahbar Jakobs Quell in einem Land voll Korn und Wein; sein Himmel träufelt Tau.
Haka Isra’ila zai zauna lafiya shi kaɗai; zuriyar Yaƙub a tsare a ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi, inda sammai za su zuba raɓa.
29 Heil dir, du Israel! Wer ist wie du? Ein Volk, so siegreich durch den Herrn! Er ist der Schild, der dich beschützt, und er das Schwert, das Siege dir erkämpft. Vor dir sich beugen deine Feinde, du schreitest über ihre Höhen hin."
Kai mai albarka ne, ya Isra’ila! Wane ne yake kamar ka, mutanen da Ubangiji ya ceta? Shi ne mafakarka da mai taimakonka da kuma takobinka mai ɗaukaka. Abokan gābanka za su zo neman jinƙai a gabanka, za ka kuwa tattake masujadansu.”

< 5 Mose 33 >