< Psalm 72 >

1 Für Salomo. O Gott, gib dem Könige deine Gerichte, und deine Gerechtigkeit dem Sohne des Königs!
Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
2 Er wird dein Volk richten in Gerechtigkeit, und deine Elenden nach Recht.
Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
3 Es werden dem Volke Frieden tragen die Berge und die Hügel durch Gerechtigkeit.
Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
4 Er wird Recht schaffen den Elenden des Volkes; er wird retten die Kinder des Armen, und den Bedrücker wird er zertreten.
Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
5 Man wird dich fürchten von Geschlecht zu Geschlecht, so lange Sonne und Mond bestehen.
Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
6 Er wird herabkommen wie ein Regen auf die gemähte Flur, wie Regenschauer, Regengüsse auf das Land.
Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
7 In seinen Tagen wird der Gerechte blühen, und Fülle von Frieden wird sein, bis der Mond nicht mehr ist.
A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
8 Und er wird herrschen von Meer zu Meer, und vom Strome bis an die Enden der Erde.
Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
9 Vor ihm werden sich beugen die Bewohner der Wüste, und seine Feinde werden den Staub lecken;
Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
10 die Könige von Tarsis und von den Inseln werden Geschenke entrichten, es werden Abgaben darbringen die Könige von Scheba und Seba.
Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
11 Und alle Könige werden vor ihm niederfallen, alle Nationen ihm dienen.
Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
12 Denn erretten wird er den Armen, der um Hilfe ruft, und den Elenden, der keinen Helfer hat;
Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
13 Er wird sich erbarmen des Geringen und des Armen, und die Seelen der Armen wird er retten.
Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
14 Von Bedrückung und Gewalttat wird er ihre Seele erlösen, und ihr Blut wird teuer sein in seinen Augen.
Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
15 Und er wird leben, und von dem Golde Schebas wird man ihm geben; und man wird beständig für ihn beten, den ganzen Tag ihn segnen.
Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
16 Es wird Überfluß an Getreide sein im Lande, auf dem Gipfel der Berge; gleich dem Libanon wird rauschen seine Frucht; und Menschen werden hervorblühen aus den Städten wie das Kraut der Erde.
Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
17 Sein Name wird ewig sein; so lange die Sonne besteht, wird fortdauern sein Name; und in ihm wird man sich segnen; alle Nationen werden ihn glücklich preisen.
Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
18 Gepriesen sei Jehova, Gott, der Gott Israels, der Wunder tut, er allein!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
19 Und gepriesen sei sein herrlicher Name in Ewigkeit! Und die ganze Erde werde erfüllt mit seiner Herrlichkeit! Amen, ja, Amen.
Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
20 Es sind zu Ende die Gebete Davids, des Sohnes Isais.
Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.

< Psalm 72 >