< Psalm 47 >
1 Dem Vorsänger. Von den Söhnen Korahs, ein Psalm. Ihr Völker alle, klatschet in die Hände! Jauchzet Gott mit Jubelschall!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
2 Denn Jehova, der Höchste, ist furchtbar, ein großer König über die ganze Erde.
Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
3 Er unterwarf uns die Völker, und die Völkerschaften unter unsere Füße.
Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
4 Er erwählte für uns unser Erbteil, den Stolz Jakobs, den er geliebt hat. (Sela)
Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
5 Gott ist emporgestiegen unter Jauchzen, Jehova unter Posaunenschall.
Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
6 Singet Gott Psalmen, singet Psalmen; singet Psalmen unserem König, singet Psalmen!
Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
7 Denn Gott ist König der ganzen Erde; singet Psalmen mit Einsicht!
Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
8 Gott regiert über die Nationen; Gott hat sich auf den Thron seiner Heiligkeit gesetzt.
Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
9 Die Edlen der Völker haben sich versammelt und das Volk des Gottes Abrahams; denn die Schilde der Erde sind Gottes; er ist sehr erhaben.
Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.