< Psalm 149 >
1 Lobet Jehova! Singet Jehova ein neues Lied, sein Lob in der Versammlung der Frommen!
Yabi Ubangiji. Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, yabonsa a cikin taron tsarkaka.
2 Israel freue sich seines Schöpfers; die Kinder Zions sollen frohlocken über ihren König!
Bari Isra’ila su yi farin ciki da Mahaliccinsu; bari mutanen Sihiyona su yi murna da Sarkinsu.
3 Loben sollen sie seinen Namen mit Reigen, mit Tamburin und Laute ihm Psalmen singen!
Bari su yabi sunansa tare da rawa suna kuma yin kiɗi gare shi da ganga da garaya.
4 Denn Jehova hat Wohlgefallen an seinem Volke; er schmückt die Sanftmütigen mit Rettung.
Gama Ubangiji yana jin daɗin mutanensa; yakan darjanta masu sauƙinkai da ceto.
5 Es sollen jubeln die Frommen in Herrlichkeit, jauchzen auf ihren Lagern!
Bari tsarkaka su yi farin ciki a wannan bangirma su kuma rera don farin ciki a kan gadajensu.
6 Lobeserhebungen Gottes seien in ihrer Kehle, und ein zweischneidiges Schwert in ihrer Hand,
Bari yabon Allah yă kasance a bakunansu takobi mai kaifi kuma a hannuwansu,
7 um Rache auszuüben an den Nationen, Bestrafungen an den Völkerschaften;
don su ɗau fansa a kan al’ummai da kuma hukunci a kan mutane,
8 ihre Könige zu binden mit Ketten, und ihre Edlen mit eisernen Fesseln;
don su ɗaura sarakuna da sarƙoƙi, manyan garinsu da sarƙoƙin ƙarfe,
9 an ihnen auszuüben das geschriebene Gericht! Das ist die Ehre aller seiner Frommen. Lobet Jehova!
don su yi hukuncin da aka rubuta a kansu. Wannan ne ɗaukakar dukan tsarkakansa. Yabi Ubangiji.