< Psalm 139 >
1 Dem Vorsänger. Von David, ein Psalm. Jehova! Du hast mich erforscht und erkannt.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
2 Du kennst mein Sitzen und mein Aufstehen, du verstehst meine Gedanken von ferne.
Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
3 Du sichtest mein Wandeln und mein Liegen und bist vertraut mit allen meinen Wegen.
Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
4 Denn das Wort ist noch nicht auf meiner Zunge, siehe, Jehova, du weißt es ganz.
Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
5 Von hinten und von vorn hast du mich eingeengt, und auf mich gelegt deine Hand.
Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
6 Kenntnis, zu wunderbar für mich, zu hoch: ich vermag sie nicht zu erfassen!
Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
7 Wohin sollte ich gehen vor deinem Geiste, und wohin fliehen vor deinem Angesicht?
Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
8 Führe ich auf zum Himmel, du bist da; und bettete ich mir in dem Scheol, siehe, du bist da. (Sheol )
In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol )
9 Nähme ich Flügel der Morgenröte, ließe ich mich nieder am äußersten Ende des Meeres,
In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
10 auch daselbst würde deine Hand mich leiten, und deine Rechte mich fassen.
can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
11 Und spräche ich: Nur Finsternis möge mich umhüllen, und Nacht werde das Licht um mich her:
In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
12 Auch Finsternis würde vor dir nicht verfinstern, und die Nacht würde leuchten wie der Tag, die Finsternis wäre wie das Licht.
duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
13 Denn du besaßest meine Nieren; du wobest mich in meiner Mutter Leibe.
Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
14 Ich preise dich darüber, daß ich auf eine erstaunliche, ausgezeichnete Weise gemacht bin. Wunderbar sind deine Werke, und meine Seele weiß es sehr wohl.
Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
15 Nicht verhohlen war mein Gebein vor dir, als ich gemacht ward im Verborgenen, gewirkt wie ein Stickwerk in den untersten Örtern der Erde.
Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
16 Meinen Keim sahen deine Augen, und in dein Buch waren sie alle eingeschrieben; während vieler Tage wurden sie gebildet, als nicht eines von ihnen war.
Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
17 Und wie köstlich sind mir deine Gedanken, o Gott! Wie gewaltig sind ihre Summen!
Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
18 Wollte ich sie zählen, ihrer sind mehr als des Sandes. Ich erwache und bin noch bei dir.
A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
19 Möchtest du, o Gott, den Gesetzlosen töten! Und ihr Blutmenschen, weichet von mir! ...
Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
20 Sie, die dich nennen zum Verbrechen, die zu Eitlem schwören, deine Feinde.
Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
21 Hasse ich nicht, Jehova, die dich hassen, und verabscheue ich nicht, die wider dich aufstehen?
Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
22 Mit vollkommenem Hasse hasse ich sie; sie sind Feinde für mich.
Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
23 Erforsche mich, Gott, und erkenne mein Herz; prüfe mich und erkenne meine Gedanken!
Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
24 Und sieh, ob ein Weg der Mühsal bei mir ist, und leite mich auf ewigem Wege!
Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.