< Sprueche 2 >
1 Mein Sohn, wenn du meine Reden annimmst und meine Gebote bei dir verwahrst,
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2 so daß du dein Ohr auf Weisheit merken läßt, dein Herz neigst zum Verständnis;
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3 ja, wenn du dem Verstande rufst, deine Stimme erhebst zum Verständnis;
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4 wenn du ihn suchst wie Silber, und wie nach verborgenen Schätzen ihm nachspürst:
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5 dann wirst du die Furcht Jehovas verstehen und die Erkenntnis Gottes finden.
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6 Denn Jehova gibt Weisheit; aus seinem Munde kommen Erkenntnis und Verständnis.
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7 Er bewahrt klugen Rat auf für die Aufrichtigen, er ist ein Schild denen, die in Vollkommenheit wandeln;
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8 indem er die Pfade des Rechts behütet und den Weg seiner Frommen bewahrt.
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9 Dann wirst du Gerechtigkeit verstehen und Recht und Geradheit, jede Bahn des Guten.
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
10 Denn Weisheit wird in dein Herz kommen, und Erkenntnis wird deiner Seele lieblich sein;
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
11 Besonnenheit wird über dich wachen, Verständnis dich behüten:
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
12 um dich zu erretten von dem bösen Wege, von dem Manne, der Verkehrtes redet;
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
13 die da verlassen die Pfade der Geradheit, um auf den Wegen der Finsternis zu wandeln;
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
14 die sich freuen, Böses zu tun, über boshafte Verkehrtheit frohlocken;
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
15 deren Pfade krumm sind, und die abbiegen in ihren Bahnen:
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
16 um dich zu erretten von dem fremden Weibe, von der Fremden, die ihre Worte glättet;
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
17 welche den Vertrauten ihrer Jugend verläßt und den Bund ihres Gottes vergißt.
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
18 Denn zum Tode sinkt ihr Haus hinab, und ihre Bahnen zu den Schatten;
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19 alle, die zu ihr eingehen, kehren nicht wieder und erreichen nicht die Pfade des Lebens:
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
20 Damit du wandelst auf dem Wege der Guten und die Pfade der Gerechten einhältst.
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
21 Denn die Aufrichtigen werden das Land bewohnen, und die Vollkommenen darin übrigbleiben;
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
22 aber die Gesetzlosen werden aus dem Lande ausgerottet, und die Treulosen daraus weggerissen werden.
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.