< Job 4 >
1 Und Eliphas, der Temaniter, antwortete und sprach:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 Wenn man ein Wort an dich versucht, wird es dich verdrießen? Doch die Worte zurückzuhalten, wer vermöchte es?
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3 Siehe, du hast viele unterwiesen, und erschlaffte Hände stärktest du;
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4 den Strauchelnden richteten deine Worte auf, und sinkende Knie hast du befestigt.
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 Doch nun kommt es an dich, und es verdrießt dich; es erreicht dich, und du bist bestürzt.
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 Ist nicht deine Gottesfurcht deine Zuversicht, die Vollkommenheit deiner Wege deine Hoffnung?
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
7 Gedenke doch: Wer ist als Unschuldiger umgekommen, und wo sind Rechtschaffene vertilgt worden?
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 So wie ich es gesehen habe: die Unheil pflügen und Mühsal säen, ernten es.
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 Durch den Odem Gottes kommen sie um, und durch den Hauch seiner Nase vergehen sie.
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10 Das Brüllen des Löwen und des Brüllers Stimme sind verstummt, und die Zähne der jungen Löwen sind ausgebrochen;
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11 der Löwe kommt um aus Mangel an Raub, und die Jungen der Löwin werden zerstreut.
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
12 Und zu mir gelangte verstohlen ein Wort, und mein Ohr vernahm ein Geflüster davon.
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13 In Gedanken, welche Nachtgesichte hervorrufen, wenn tiefer Schlaf die Menschen befällt,
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14 kam Schauer über mich und Beben, und durchschauerte alle meine Gebeine;
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15 und ein Geist zog vor meinem Angesicht vorüber, das Haar meines Leibes starrte empor.
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 Es stand da, und ich erkannte sein Aussehen nicht; ein Bild war vor meinen Augen, ein Säuseln und eine Stimme hörte ich:
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 Sollte ein Mensch gerechter sein als Gott, oder ein Mann reiner als der ihn gemacht hat?
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 Siehe, auf seine Knechte vertraut er nicht, und seinen Engeln legt er Irrtum zur Last:
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 wieviel mehr denen, die in Lehmhäusern wohnen, deren Grund im Staube ist! Wie Motten werden sie zertreten.
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
20 Von Morgen bis Abend werden sie zerschmettert; ohne daß man's beachtet, kommen sie um auf ewig.
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
21 Ist es nicht so? Wird ihr Zeltstrick an ihnen weggerissen, so sterben sie, und nicht in Weisheit.
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’