< Psalm 81 >

1 [Dem Vorsänger, auf der Gittith. Von Asaph.] Jubelt Gott, unserer Stärke! jauchzet dem Gott Jakobs!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 Erhebet Gesang und lasset das Tamburin ertönen, die liebliche Laute samt der Harfe!
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 Stoßet am Neumonde in die Posaune, am Vollmonde zum Tage unseres Festes!
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 Denn eine Satzung für Israel ist es, eine Verordnung des Gottes Jakobs.
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 Er setzte es ein als ein Zeugnis in Joseph, als er auszog gegen das Land Ägypten, wo ich eine Sprache hörte, die ich nicht kannte.
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 Ich entzog der Last seine Schulter, seine Hände entgingen dem Tragkorbe.
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 In der Bedrängnis riefest du, und ich befreite dich; ich antwortete dir in des Donners Hülle; [Eig. Verborgenheit] ich prüfte dich an den Wassern von Meriba. (Sela)
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 Höre, mein Volk, und ich will wider dich zeugen. O Israel, wenn du mir gehorchtest!
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 Es soll kein fremder Gott [El] unter dir sein, und du sollst dich nicht bücken vor einem Gott [El] des Auslandes.
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 Ich bin Jehova, dein Gott, der dich aus dem Lande Ägypten heraufgeführt hat; tue deinen Mund weit auf, und ich will ihn füllen.
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 Aber mein Volk hat nicht auf meine Stimme gehört, und Israel ist nicht willig gegen mich gewesen.
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 Und ich gab sie dahin der Verstocktheit ihres Herzens; sie wandelten nach ihren Ratschlägen.
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 O daß mein Volk auf mich gehört, daß Israel in meinen Wegen gewandelt hätte!
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 Bald würde ich ihre Feinde gebeugt und meine Hand gewendet haben gegen ihre Bedränger.
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 Die Hasser Jehovas würden sich ihm mit Schmeichelei unterworfen haben [S. die Anm. zu Ps. 18,44,] und ihre Zeit würde ewig gewesen sein;
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 Und mit dem Fette des Weizens würde er [And. l.: ich] es gespeist, und mit Honig aus dem Felsen würde ich dich gesättigt haben.
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”

< Psalm 81 >