< Psalm 55 >
1 [Dem Vorsänger, mit Saitenspiel. Ein Maskil [S. die Anm. zu Ps. 32, Überschrift] von David.] Nimm zu Ohren, o Gott, mein Gebet, und verbirg dich nicht vor meinem Flehen!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
2 Horche auf mich und antworte mir! Ich irre umher in meiner Klage und muß stöhnen
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
3 Vor der Stimme des Feindes, vor der Bedrückung des Gesetzlosen; denn sie wälzen Unheil auf mich, und im Zorn feinden sie mich an.
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
4 Mein Herz ängstigte sich in meinem Innern, und Todesschrecken haben mich befallen.
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
5 Furcht und Zittern kamen mich an, und Schauder bedeckte mich.
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
6 Und ich sprach: O daß ich Flügel hätte wie die Taube! Ich wollte hinfliegen und ruhen.
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
7 Siehe, weithin entflöhe ich, würde weilen in der Wüste. (Sela)
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
8 Ich wollte eilends entrinnen vor dem heftigen Winde, vor dem Sturme.
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
9 Vernichte, Herr, zerteile ihre Zunge! [d. h. vereitle ihren Ratschlag] denn Gewalttat und Hader habe ich in der Stadt gesehen.
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
10 Tag und Nacht machen sie die Runde um sie auf ihren Mauern; und Unheil und Mühsal [O. Frevel und Unrecht] sind in ihrer Mitte.
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
11 Schadentun ist in ihrer Mitte, und Bedrückung und Trug weichen nicht von ihrer Straße. [O. ihrem Markte]
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
12 Denn nicht ein Feind ist es, der mich höhnt, sonst würde ich es ertragen; nicht mein Hasser ist es, der wider mich großgetan hat, sonst würde ich mich vor ihm verbergen;
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
13 sondern du, ein Mensch meinesgleichen, mein Freund und mein Vertrauter;
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
14 die wir trauten Umgang miteinander pflogen, ins Haus Gottes wandelten mit der Menge.
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
15 Der Tod überrasche sie, [Nach and. Lesart: Verwüstung über sie!] lebendig mögen sie hinabfahren in den Scheol! denn Bosheiten sind in ihrer Wohnung, in ihrem Innern. (Sheol )
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol )
16 Ich aber, ich rufe zu Gott, und Jehova rettet mich.
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17 Abends und morgens und mittags muß ich klagen und stöhnen, und er hört meine Stimme.
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18 Er hat meine Seele in Frieden erlöst aus dem Kampfe wider mich; [O. daß sie mir nicht nahten] denn ihrer sind viele gegen mich gewesen.
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19 Hören wird Gott [El] und sie demütigen, [O. ihnen antworten] -er thront ja von alters her (Sela) -weil es keine Änderung bei ihnen [O. sie, bei denen es keine usw.] gibt und sie Gott nicht fürchten.
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20 Er [d. h. der Gesetzlose] hat seine Hände ausgestreckt gegen die, welche mit ihm in Frieden waren; seinen Bund hat er gebrochen. [Eig. entweiht]
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21 Glatt sind die Milchworte seines Mundes, und Krieg ist sein Herz; geschmeidiger sind seine Worte als Öl, und sie sind gezogene Schwerter.
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22 Wirf auf Jehova, was dir auferlegt [O. beschieden] ist, und er wird dich erhalten; er wird nimmermehr zulassen, daß der Gerechte wanke!
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
23 Und du, Gott, wirst sie hinabstürzen in die Grube des Verderbens; die Männer des Blutes und des Truges werden nicht zur Hälfte bringen ihre Tage. Ich aber werde auf dich vertrauen.
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.