< Psalm 17 >

1 [Ein Gebet; von David.] Höre, Jehova, die Gerechtigkeit, horche auf mein Schreien; nimm zu Ohren mein Gebet von Lippen ohne Trug!
Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
2 Von deiner Gegenwart gehe mein Recht aus; laß deine Augen Aufrichtigkeit anschauen!
Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
3 Du hast mein Herz geprüft, hast mich des Nachts durchforscht; du hast mich geläutert-nichts fandest du; mein Gedanke geht nicht weiter als mein Mund.
Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
4 Was das Tun des Menschen anlangt, so habe ich [O. Beim Tun des Menschen habe ich usw.] mich durch das Wort deiner Lippen bewahrt vor den Wegen des Gewalttätigen.
Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
5 Meine Schritte hielten fest an deinen Spuren, meine Tritte haben nicht gewankt.
Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
6 Ich, ich habe dich angerufen, denn du erhörest mich, o Gott. [El] Neige dein Ohr zu mir, höre meine Rede!
Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
7 Erweise wunderbar deine Gütigkeiten, der du durch deine Rechte die auf dich Trauenden [O. der du die auf deine Rechte Trauenden usw.] rettest vor denen, die sich wider sie erheben.
Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
8 Bewahre mich wie den Augapfel im Auge; [Eig. den Augapfel, den Augenstern] birg mich in dem Schatten deiner Flügel
Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
9 Vor den Gesetzlosen, die mich zerstören, meinen Todfeinden, die mich umzingeln.
daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
10 Ihr fettes Herz verschließen sie, mit ihrem Munde reden sie stolz. [W. in Hoffart]
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11 In allen unseren Schritten haben sie uns jetzt umringt; sie richten ihre Augen, uns zu Boden zu strecken.
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12 Er ist gleich einem Löwen, der nach Raub schmachtet, [Eig. der gierig ist zu zerfleischen] und wie ein junger Löwe, sitzend im Versteck.
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
13 Stehe auf, Jehova! komm ihm zuvor, [O. tritt ihm entgegen] wirf ihn nieder! Errette meine Seele von dem Gesetzlosen durch dein Schwert; [And.: dem Gesetzlosen, deinem Schwerte]
Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
14 Von den Leuten durch deine Hand, [And.: den Leuten deiner Hand] Jehova, von den Leuten dieses Zeitlaufs! Ihr Teil ist in diesem Leben, und ihren Bauch füllst du mit deinem Schatze; sie haben Söhne die Fülle, und ihren Überfluß lassen sie ihren Kindern.
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
15 Ich, ich werde dein Angesicht schauen in Gerechtigkeit, werde gesättigt werden, wenn ich erwache, mit deinem Bilde.
Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.

< Psalm 17 >