< Sprueche 7 >

1 Mein Sohn, bewahre meine Worte, und birg bei dir meine Gebote;
Ɗana, ka kiyaye kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka.
2 bewahre meine Gebote und lebe, und meine Belehrung wie deinen Augapfel.
Ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu; ka tsare koyarwata kamar ƙwayar idonka.
3 Binde sie um deine Finger, schreibe sie auf die Tafel deines Herzens.
Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.
4 Sprich zur Weisheit: Du bist meine Schwester! und nenne den Verstand deinen Verwandten;
Ka faɗa wa hikima, “Ke’yar’uwata ce,” ka kuma kira fahimi danginka;
5 damit sie dich bewahre vor dem fremden Weibe, vor der Fremden, [Eig. Ausländerin] die ihre Worte glättet. -
za su kiyaye ka daga mazinaciya, daga mace marar aminci da kalmominta masu ɗaukan hankali.
6 Denn an dem Fenster meines Hauses schaute ich durch mein Gitter hinaus;
A tagar gidana na leƙa ta labule mai rammuka.
7 und ich sah unter den Einfältigen, gewahrte unter den Söhnen einen unverständigen [Eig. des Verstandes bar; so auch Kap. 6,32;9,4;10,13 und öfter] Jüngling,
Sai na gani a cikin marasa azanci, na lura a cikin samari, wani matashi wanda ba shi da hankali.
8 der hin und her ging auf der Straße, neben ihrer Ecke, und den Weg nach ihrem Hause schritt,
Yana gangarawa a titi kusa da kusurwarta, yana tafiya a gefen wajen gidanta
9 in der Dämmerung, am Abend des Tages, in der Mitte der Nacht und in der Dunkelheit.
da magariba, yayinda rana tana fāɗuwa, yayinda duhun dare yana farawa.
10 Und siehe, ein Weib kam ihm entgegen im Anzug einer Hure und mit verstecktem Herzen. -
Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
11 Sie ist leidenschaftlich und unbändig, ihre Füße bleiben nicht in ihrem Hause;
(Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
12 bald ist sie draußen, bald auf den Straßen, und neben jeder Ecke lauert sie. -
wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
13 Und sie ergriff ihn und küßte ihn, und mit unverschämtem Angesicht sprach sie zu ihm:
Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
14 Friedensopfer lagen mir ob, heute habe ich meine Gelübde bezahlt;
“Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
15 darum bin ich ausgegangen, dir entgegen, um dein Antlitz zu suchen, und dich habe dich gefunden.
Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
16 Mit Teppichen habe ich mein Bett bereitet, mit bunten Decken von ägyptischem Garne;
Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
17 ich habe mein Lager benetzt mit Myrrhe, Aloe und Zimmet.
Na yayyafa turare a gadona da mur, aloyes da kuma kirfa.
18 Komm, wir wollen uns in Liebe berauschen bis an den Morgen, an Liebkosungen uns ergötzen.
Zo, mu sha zurfin ƙauna har safe; bari mu ji wa ranmu daɗi da ƙauna!
19 Denn der Mann ist nicht zu Hause, er ist auf eine weite Reise gegangen;
Mijina ba ya gida; ya yi tafiya mai nisa.
20 er hat den Geldbeutel in seine Hand genommen, am Tage des Vollmondes wird er heimkehren.
Ya ɗauki jakarsa cike da kuɗi ba zai kuwa dawo gida ba sai tsakiyar wata.”
21 Sie verleitete ihn durch ihr vieles Bereden, riß ihn fort durch die Glätte ihrer Lippen.
Da kalmomin rarrashi ta sa ya kauce; ta ɗauki hankalinsa da sulɓin maganarta.
22 Auf einmal ging er ihr nach, wie ein Ochs zur Schlachtbank geht, und wie Fußfesseln zur Züchtigung des Narren dienen, [Wahrsch. ist zu l.: und ein Narr zur Züchtigung in Fußfesseln]
Nan take, ya bi ta kamar saniyar da za a kai mayanka, kamar wawa zuwa wurin da za a ba shi horo
23 bis ein Pfeil seine Leber zerspaltet; wie ein Vogel zur Schlinge eilt und nicht weiß, daß es sein Leben gilt. -
sai da kibiya ta soki hantarsa, kamar tsuntsun da ya ruga cikin tarko, ba tare da sani zai zama sanadin ransa ba.
24 Nun denn, ihr Söhne, höret auf mich, und horchet auf die Worte meines Mundes!
Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; ku kasa kunne ga abin da nake faɗa.
25 Dein Herz wende sich nicht ab nach ihren Wegen, und irre nicht umher auf ihren Pfaden!
Kada ku bar zuciyarku ta juya zuwa hanyoyinta ko ku kauce zuwa hanyoyinta.
26 Denn viele Erschlagene hat sie niedergestreckt, und zahlreich sind alle ihre Ermordeten.
Ta zama sanadin fāɗuwar yawanci; kisan da ta yi ba ta ƙidayuwa.
27 Ihr Haus sind Wege zum Scheol, die hinabführen zu den Kammern des Todes. (Sheol h7585)
Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol h7585)

< Sprueche 7 >