< Nehemia 7 >

1 Und es geschah, als die Mauer gebaut war, da setzte ich die Türflügel ein; und die Torhüter und die Sänger und die Leviten wurden bestellt.
Bayan an sāke gina katangar na kuma sa ƙofofi a wurarensu, sai aka naɗa masu tsaro, da mawaƙa, da Lawiyawa.
2 Und ich beorderte über Jerusalem meinen Bruder Hanani und Hananja, den Obersten der Burg; denn er war ein sehr treuer Mann und gottesfürchtig vor vielen.
Na sa ɗan’uwana Hanani tare da Hananiya shugaban fada aikin riƙon Urushalima, domin shi Hananiya mutum mai mutunci ne, mai tsoron Allah fiye da yawancin mutane.
3 Und ich sprach zu ihnen: Die Tore Jerusalems sollen nicht eher geöffnet werden, als bis die Sonne heiß scheint; und während sie [die Wachen] noch dastehen, soll man die Türflügel zumachen, und verschließet sie. Und ihr sollt Wachen aus den Bewohnern Jerusalems aufstellen, den einen auf seine Wache und den anderen vor sein Haus.
Na ce musu, “Kada a buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe sai rana ta fito sosai. Yayinda matsaran ƙofofi suna aiki, a kulle ƙofofin a sa musu sakata kafin matsaran su tashi, wajen fāɗuwar rana. Ku kuma naɗa mazaunan Urushalima a matsayin masu tsaro, waɗansunsu a wuraren aiki, waɗansun kuma kusa da gidajensu.”
4 Die Stadt aber war geräumig [Eig. weit nach allen Seiten hin] und groß, und das Volk darin spärlich, und keine Häuser waren gebaut.
Birnin Urushalima kuwa tana da fāɗi da girma, amma mutanen da suke zama a cikinta kaɗan ne, ba a kuma gina gidaje da yawa ba tukuna.
5 Und mein Gott gab mir ins Herz, die Edlen und die Vorsteher und das Volk zu versammeln, um sie nach den Geschlechtern zu verzeichnen. Und ich fand das Geschlechtsverzeichnis derer, die zuerst heraufgezogen waren, und fand darin geschrieben:
Sai Allahna ya sa a zuciyata in tara manyan gari, shugabanni da talakawa don a rubuta su bisa ga iyalansu. Na sami littafin asali na waɗanda suka fara dawowa. Ga abin da na tarar an rubuta a ciki.
6 Dies [Vergl. Esra 2] sind die Kinder der Landschaft Juda, welche aus der Gefangenschaft der Weggeführten, die Nebukadnezar, der König von Babel, weggeführt hatte, hinaufzogen, und die nach Jerusalem und Juda zurückkehrten, ein jeder in seine Stadt,
Waɗannan su ne mutanen yankin da suka dawo daga zaman bautar da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kame (sun dawo Urushalima da Yahuda, kowanne zuwa garinsa.
7 welche kamen mit Serubbabel, Jeschua, Nehemia, Asarja, Raamja, Nachamani, Mordokai, Bilschan, Mispereth, Bigwai, Nechum, Baana. Zahl der Männer des Volkes Israel:
Sun dawo tare da Zerubbabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Azariya, da Ra’amiya, da Nahamani, da Mordekai, da Bilshan, da Misfar, da Bigwai, da Nehum da kuma Ba’ana). Ga jerin mutanen Isra’ila.
8 Die Söhne Parhosch, 2172;
Zuriyar Farosh mutum 2,172
9 die Söhne Schephatjas, 372;
ta Shefatiya 372
10 die Söhne Arachs, 652;
ta Ara 652
11 die Söhne Pachath-Moabs, von den Söhnen Jeschuas und Joabs, 2818;
ta Fahat-Mowab (ta wurin Yeshuwa da Yowab) 2,818
12 die Söhne Elams, 1254;
ta Elam 1,254
13 die Söhne Sattus, 845;
ta Zattu 845
14 die Söhne Sakkais, 760;
ta Zakkai 760
15 die Söhne Binnuis, 648;
ta Binnuyi 648
16 die Söhne Bebais, 628;
ta Bebai 628
17 die Söhne Asgads, 2322;
ta Azgad 2,322
18 die Söhne Adonikams, 667;
ta Adonikam 667
19 die Söhne Bigwais, 2067;
ta Bigwai 2,067
20 die Söhne Adins, 655;
ta Adin 655
21 die Söhne Aters, von Hiskia, 98;
ta Ater (ta wurin Hezekiya) 98
22 die Söhne Haschums, 328;
ta Hashum 328
23 die Söhne Bezais, 324;
ta Bezai 324
24 die Söhne Hariphs, 112;
ta Harif 112
25 die Söhne Gibeons, 95;
ta Gibeyon 95.
26 die Männer von Bethlehem und Netopha, 188;
Mutanen Betlehem da na Netofa 188
27 die Männer von Anathoth, 128;
na Anatot 128
28 die Männer von Beth-Asmaweth, 42;
na Bet-Azmawet 42
29 die Männer von Kirjath-Jearim, Kephira und Beeroth, 743;
na Kiriyat Yeyarim, Kefira da na Beyerot 743
30 die Männer von Rama und Geba, 621;
na Rama da na Geba 621
31 die Männer von Mikmas, 122;
na Mikmash 122
32 die Männer von Bethel und Ai, 123;
na Betel da na Ai 123
33 die Männer von dem anderen Nebo, [Wahrsch. ist zu lesen: von Nebo] 52;
na ɗayan Nebo 52
34 die Söhne des anderen [S. v 12] Elam, 1254;
na ɗayan Elam 1,254
35 die Söhne Harims, 320;
na Harim 2 320
36 die Söhne Jerechos, 345;
na Yeriko 345
37 die Söhne Lods, Hadids und Onos, 721;
na Lod, da na Hadid, da na Ono 721
38 die Söhne Senaas, 3930.
na Sena’a 3,930.
39 Die Priester: die Söhne Jedajas, vom Hause Jeschuas, 973;
Ga zuriyar Firistoci. Zuriyar Yedahiya (ta wurin iyalin Yeshuwa) 973
40 die Söhne Immers, 1052;
ta Immer 1,052
41 die Söhne Paschchurs, 1247;
ta Fashhur 1,247
42 die Söhne Harims, 1017.
ta Harim 1,017.
43 Die Leviten: die Söhne Jeschuas und Kadmiels, von den Söhnen Hodwas, [Nach and. L.: Hodawjas] 74. -
Ga zuriyar Lawiyawa. Zuriyar Yeshuwa da Kadmiyel (ta wurin Hodeba) 74.
44 Die Sänger: die Söhne Asaphs, 148. -
Mawaƙa. Zuriyar Asaf mutum 148.
45 Die Torhüter: die Söhne Schallums, die Söhne Aters, die Söhne Talmons, die Söhne Akkubs, die Söhne Hatitas, die Söhne Schobais, 138.
Ga zuriyar Matsaran Ƙofofi. Zuriyar Shallum, Ater, Talmon, Akkub, Hatita da Shobai 138.
46 Die Nethinim: die Söhne Zichas, die Söhne Hasuphas, die Söhne Tabbaoths,
Ma’aikatan haikali. Zuriyar Ziha, Hasufa, Tabbawot,
47 die Söhne Keros, die Söhne Sias, die Söhne Padons,
da ta Keros, da ta Siya, da ta Fadon,
48 die Söhne Lebanas, die Söhne Hagabas, die Söhne Salmais,
da ta Lebana, da ta Hagaba, da ta Shalmai,
49 die Söhne Hanans, die Söhne Giddels, die Söhne Gachars,
da ta Hanan, da ta Giddel, da ta Gahar,
50 die Söhne Reajas, die Söhne Rezins, die Söhne Nekodas,
da ta Reyahiya, da ta Rezin, da ta Nekoda,
51 die Söhne Gassams, die Söhne Ussas, die Söhne Paseachs,
da ta Gazzam, da ta Uzza, da ta Faseya,
52 die Söhne Besais, die Söhne der Meunim, [d. h. der Meuniter; [Maoniter]] die Söhne der Nephisim, [Nach and. L.: Nephusim]
da ta Besai, da ta Meyunawa, da ta Nefussiyawa,
53 die Söhne Bakbuks, die Söhne Hakuphas, die Söhne Harchurs,
da ta Bakbuk, da ta Hakufa, da ta Harhur,
54 die Söhne Bazluths, [Nach and. L.: Bazliths] die Söhne Mechidas, die Söhne Harschas,
da ta Bazlit, da ta Mehida, da ta Harsha,
55 die Söhne Barkos, die Söhne Siseras, die Söhne Tamachs,
da ta Barkos, da ta Sisera, da ta Tema,
56 die Söhne Neziachs, die Söhne Hatiphas.
da ta Neziya, da kuma ta Hatifa.
57 Die Söhne der Knechte Salomos: die Söhne Sotais, die Söhne Sophereths, die Söhne Peridas,
Ga zuriyar bayin Solomon. Zuriyar Sotai, da ta Soferet, da ta Ferida,
58 die Söhne Jaalas, die Söhne Darkons, die Söhne Giddels,
da ta Ya’ala, da ta Darkon, da ta Giddel,
59 die Söhne Schephatjas, die Söhne Hattils, die Söhne Pokereths-Hazzebaim, die Söhne Amons.
Shefatiya, Hattil, Fokeret-Hazzebayim, da Amon.
60 Alle Nethinim und Söhne der Knechte Salomos: 392.
Zuriyar ma’aikatan haikali da ta bayin Solomon su 392.
61 Und diese sind es, die aus Tel-Melach, Tel-Harscha, Kerub, Addon und Immer hinaufzogen; aber sie konnten ihr Vaterhaus und ihre Abkunft [Eig. ihren Samen] nicht angeben, ob sie aus Israel wären:
Waɗansu sun hauro daga garuruwan Tel-Mela, Tel-Harsha, Kerub, Addon da Immer, amma ba su iya nuna cewa iyalansu su zuriyar Isra’ila ce ba,
62 die Söhne Delajas, die Söhne Tobijas, die Söhne Nekodas, 642.
zuriyar Delahiya, Tobiya, da Nekoda 642.
63 Und von den Priestern: die Söhne Habajas, die Söhne Hakkoz, die Söhne Barsillais, der ein Weib von den Töchtern Barsillais, des Gileaditers, genommen hatte und nach ihrem Namen genannt wurde.
Na wajen firistoci kuwa su ne, Zuriyar Hobahiya, da ta Hakkoz, da ta Barzillai (wani mutumin da ya auri’yar Barzillai mutumin Gileyad, aka kuma kira shi da wannan suna).
64 Diese suchten ihr Geschlechtsregisterverzeichnis, aber es wurde nicht gefunden; und sie wurden von dem Priestertum als unrein ausgeschlossen.
Waɗannan ne aka nemi sunayensu a cikin tarihin asalin iyalai, amma ba a same su a ciki ba, saboda haka aka hana su shiga cikin firistoci, sun zama kamar marasa tsarki.
65 Und der Tirsatha [S. die Anm. zu Esra 2,63] sprach zu ihnen, daß sie von dem Hochheiligen nicht essen dürften, bis ein Priester für die Urim und die Thummim aufstände.
Sai gwamna ya umarce su kada su ci wani abinci mafi tsarki, sai akwai firist da zai nemi nufin Ubangiji ta wurin Urim da Tummim.
66 Die ganze Versammlung insgesamt war 42360,
Yawan jama’ar duka ya kai mutum 42,360,
67 außer ihren Knechten und ihren Mägden; dieser waren 7337. Und sie hatten 245 Sänger und Sängerinnen.
ban da bayinsu maza da mata 7,337. Suna kuma da mawaƙa maza da mata 245.
68 Ihrer Rosse waren 736, ihrer Maultiere 245,
Akwai dawakai 736, alfadarai 245
69 der Kamele 435, der Esel 6720.
raƙuma 435, da kuma jakuna 6,720.
70 Und ein Teil der Häupter der Väter gab zum Werke. Der Tirsatha gab für den Schatz: an Gold 1000 Dariken, [S. die Anm. zu 1. Chron. 29,7] 50 Sprengschalen, 530 Priesterleibröcke.
Waɗansu shugabannin iyalai suka ba da kyautai domin taimakon aiki. Gwamna ya ba da darik 1,000 na zinariya, kwanoni 50, da riguna 530 don firistoci.
71 Und einige von den Häuptern der Väter gaben für den Schatz des Werkes: an Gold 20000 Dariken, und an Silber 2200 Minen.
Waɗansu shugabannin iyalai sun ba da darik 20,000 na zinariya da mina 2,200 na azurfa don aiki.
72 Und was das übrige Volk gab, war an Gold 20000 Dariken, und an Silber 2000 Minen, und 67 Priesterleibröcke.
Jimillar da sauran mutane suka bayar ta kai darik 20,000 na zinariya, minas 2,000 na azurfa, da riguna sittin da bakwai don firistoci.
73 Und die Priester und die Leviten und die Torhüter und die Sänger und die aus dem Volke und die Nethinim und ganz Israel wohnten in ihren Städten.
Firistoci, da Lawiyawa, da matsaran ƙofofi, da mawaƙa, da ma’aikatan haikali tare da waɗansu mutane da kuma sauran mutanen Isra’ila, suka zauna a garuruwansu. Da wata na bakwai ya zo, Isra’ilawa kuwa sun riga sun zauna a garuruwansu,

< Nehemia 7 >