< Job 13 >
1 Siehe, das alles hat mein Auge gesehen, mein Ohr gehört und sich gemerkt.
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 So viel ihr wisset, weiß auch ich; ich stehe nicht hinter euch zurück.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 Doch zu dem Allmächtigen will ich reden, und vor Gott [El] mich zu rechtfertigen begehre ich;
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 ihr hingegen seid Lügenschmiede, nichtige Ärzte, ihr alle!
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 O daß ihr doch stille schwieget! das würde euch zur Weisheit gereichen.
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Höret doch meine Rechtfertigung, und horchet auf die Beweisgründe meiner Lippen!
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 Wollt ihr für Gott [El] Unrecht reden, und für ihn Trug reden?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 Wollt ihr für ihn Partei nehmen? oder wollt ihr für Gott [El] rechten?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 Ist es gut für euch, daß er euch erforsche? oder werdet ihr ihn täuschen, wie man einen Menschen täuscht?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 Strafen wird er euch, wenn ihr im Geheimen die Person ansehet.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 Wird nicht seine Hoheit euch bestürzen, und sein Schrecken auf euch fallen?
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 Eure Denksprüche sind Sprüche von Asche, eure Schutzwehren erweisen sich als Schutzwehren von Lehm.
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 Schweiget, laßt mich, und ich will reden, was auch über mich ergehen möge.
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 Warum sollte ich mein Fleisch zwischen meine Zähne nehmen, und mein Leben meiner Hand anvertrauen? [O. wie anderswo: mein Leben aufs Spiel setzen]
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 Siehe, tötet er mich, ich werde auf ihn warten, [O. hoffen. Nach and. Les.: Siehe er will mich töten, ich habe nichts zu hoffen] nur will ich meine Wege ihm ins Angesicht rechtfertigen.
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 Auch das wird mir zur Rettung sein, daß ein Ruchloser nicht vor sein Angesicht kommen darf.
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 Höret, höret meine Rede, und meine Erklärung dringe in eure Ohren!
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 Siehe doch, ich habe die Rechtssache gerüstet! Ich weiß, daß ich Recht behalten werde.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 Wer ist es, der mit mir rechten könnte? Denn dann wollte ich schweigen und verscheiden.
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 Nur zweierlei tue mir nicht; dann werde ich mich nicht vor deinem Angesicht verbergen.
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 Deine Hand entferne von mir, und dein Schrecken ängstige mich nicht.
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 So rufe denn, und ich will antworten, oder ich will reden, und erwidere mir!
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 Wie viele Missetaten und Sünden habe ich? Laß mich meine Übertretung und meine Sünde wissen!
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 Warum verbirgst du dein Angesicht, und hältst mich für deinen Feind?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 Willst du ein verwehtes Blatt hinwegschrecken, und die dürre Stoppel verfolgen?
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 Denn Bitteres verhängst [Eig. schreibst, verfügst] du über mich, und lässest mich erben die Missetaten meiner Jugend;
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 und meine Füße legst du in den Stock, und beobachtest alle meine Pfade, grenzest dir ein die Sohlen meiner Füße;
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 da ich doch zerfalle [Eig. da er doch zerfällt; nämlich der vorher beschriebene Mann] wie Moder, wie ein Kleid, das die Motte zerfressen hat.
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.