< Job 12 >

1 Und Hiob antwortete und sprach:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Fürwahr, ihr seid die Leute, und mit euch wird die Weisheit aussterben!
“Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
3 Auch ich habe Verstand wie ihr; ich stehe nicht hinter euch zurück; [Eig. ich falle nicht gegen euch ab; so auch Kap. 13,2] und wer wüßte nicht dergleichen?
Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
4 Ich muß einer sein, der seinem Freunde zum Gespött ist, der zu Gott ruft, und er antwortet [O. rief antwortete] ihm; der Gerechte, Vollkommene ist zum Gespött!
“Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
5 Dem Unglück gebührt Verachtung nach den Gedanken des Sorglosen; sie ist bereit für die, welche mit dem Fuße wanken.
Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
6 Die Zelte der Verwüster sind in Ruhe, und Sicherheit ist für die, welche Gott [El] reizen, für den, welcher Gott in seiner Hand führt. [d. h. welcher nur auf seine Hand vertraut. Vergl. Hab. 1,11]
Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
7 Aber frage doch das Vieh, und es wirds dich lehren; und das Gevögel des Himmels, und es wirds dir kundtun;
“Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
8 oder rede zu der Erde, und sie wirds dich lehren; und die Fische des Meeres werden es dir erzählen.
Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
9 Wer erkennte nicht an diesen allen, daß die Hand Jehovas solches gemacht hat,
Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
10 in dessen Hand die Seele alles Lebendigen ist und der Geist alles menschlichen Fleisches?
Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
11 Soll nicht das Ohr die Worte prüfen, wie der Gaumen für sich die Speise kostet?
Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
12 Bei Greisen ist Weisheit, und Einsicht bei hohem Alter.
Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
13 Bei ihm ist Weisheit und Macht, sein ist Rat und Einsicht.
“Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
14 Siehe, er reißt nieder, und es wird nicht wieder gebaut; er schließt über jemand zu, und es wird nicht aufgetan.
Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
15 Siehe, er hemmt die Wasser, und sie vertrocknen; und er läßt sie los, und sie kehren das Land um.
Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
16 Bei ihm ist Kraft und vollkommenes Wissen; sein ist der Irrende und der Irreführende.
Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
17 Er führt Räte beraubt [Eig. ausgezogen] hinweg, und Richter macht er zu Narren.
Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
18 Die Herrschaft der Könige löst er auf, und schlingt eine Fessel [Eig. einen Gurt, ein Band] um ihre Lenden.
Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
19 Er führt Priester beraubt [Eig. ausgezogen] hinweg, und Feststehende stürzt er um.
Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
20 Zuverlässigen [d. h. solchen, auf deren Rat man sich verlassen kann] entzieht er die Sprache, und Alten benimmt er das Urteil.
Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
21 Verachtung schüttet er auf Edle, und den Gürtel der Starken macht er schlaff.
Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
22 Er enthüllt Tiefes aus der Finsternis, und Todesschatten zieht er an das Licht hervor.
Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
23 Er vergrößert Nationen, und er vernichtet sie; er breitet Nationen aus, und er führt sie hinweg.
yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
24 Er entzieht den Verstand den Häuptern der Völker der Erde, und macht sie umherirren in pfadloser Einöde;
Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
25 sie tappen in der Finsternis, wo kein Licht ist, und er macht sie umherirren gleich einem Trunkenen.
Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.

< Job 12 >