< Marqqossa 14 >

1 Pazigane uketh muussa ba7ale galasay bonchetanas namm7u galasi atishin qesista halaqatine Muse woga tamarsizayti Yesusa balethi oykidi wodhdana ogge koyida.
To, saura kwana biyu ne kaɗai a yi Bikin Ƙetarewa da Bikin Burodi Marar Yisti, sai manyan firistoci da malaman dokoki, suka nemi wani dalili su kama Yesu a ɓoye, su kashe.
2 Gido atin asay meto medhonta mala ha bocho ba7ale galasatan gidoppo gida.
Suka ce, “Ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su yi tawaye.”
3 Izi Biittaniya giza son issi kasse inchiracha hargi paxida Simona getetizaysa son quumma bolla dishin waagay daro al7o gidida nadorse getetiza shitoy kummi utida philqaxe ooykida issi macashaya philqaxeza menthada shitoza Yesusa hu7e bolla gusadus.
Yayinda yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu, yana cin abinci, sai wata mace ta zo da wani ɗan tulu na turaren alabasta da aka yi da nardi zalla, mai tsadan gaske. Ta fasa tulun, ta kuma zuba turaren a kansa.
4 Hen gadan diza asatappe issi issi asati “haysi shitozi aazas wogay baynda gukize?” gidi ba garsan hanqettida.
Waɗansu daga cikin waɗanda suke wurin, suka ji haushi, suka ce wa juna, “Me ya sa za a ɓata turaren nan haka?
5 Shitozi bayzo bayzidakko heedzdzu xeetu dinareppe bollara bayzetidi manqotas immistanashin, giidi macashiyokka kadhida.
Da an sayar da shi, ai, da an sami kuɗi fiye da albashi ma’aikaci na shekara guda, a ba wa matalauta. Sai suka tsawata mata da zafi.”
6 Gido atin Yesusay istas hizgidees “agitte hano macashayo aazas wayseti? Iza tass lo7o miish oothadus.
Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta mana. Don me kuke damunta? Ta yi abu mai kyau a gare ni.
7 Manqoti ay wodekka intenara detees. Inte koyda wode aydekka ista madanas danda7ista shin ta gidikko wursso wode intenara dikke.
Matalauta dai suna tare da ku kullum, za ku kuma iya taimakonsu a duk lokacin da kuke so. Amma ni ba zan kasance da ku kullum ba.
8 Hanna ba oothanas danda7izari keena oothadus. Tass mogos gidana mala ta asho kasista tiyadus.
Ta yi abin da ta iya yi. Ta zuba turare a jikina kafin lokaci, don shirin jana’izata.
9 Ta intes tummu gays haysi mishiracho qalay alame kumethan sabaketizason awankka iza othidaysi izo hassa7isizaz gididi hasa7istana.
Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bishara ko’ina a duniya, za a faɗi abin da ta yi, domin tunawa da ita.”
10 Hessappe guye tamane namm7atappe issay Asqoroto Yuday Yesusa athi immans qesista halaqatakko bidess.
Sai Yahuda Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya je wajen manyan firistoci don yă bashe Yesu a gare su.
11 Istika hessa siyidi ufa7etida, izas mishe immans izara gigida. Hessa gish Yesusa athi immanas giga wode nagishe gamm7idees.
Suka yi murna da jin haka, suka yi alkawari za su ba shi kuɗi. Don haka, ya fara neman zarafi yă ba da shi.
12 Paziga dorssi shuketiza uuketha mussa bonchiza koyro galas Yesusa kalizayti Yesusakko shiqidi “Paziga ka7o manaso awan gigisana mala koyaz?” gi oychida.
A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, lokacin da akan yanka ɗan ragon hadayar kafara, bisa ga al’ada ta tunawa da Bikin Ƙetarewa, sai almajiran Yesu suka tambaye shi, suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
13 Izikka bena kalizaytappe namm7ata hizgi kitides “Gede katama biitte, inte bishin issi hath otora tokidadaey intenara gagana.
Sai ya aiki biyu daga cikin almajiransa ya ce, “Ku shiga cikin birni, za ku sadu da wani ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi.
14 Izi bidi gelizaso gakanas iza kalitte. Keethadezas “Astamarey nena, tana kalizaytara paziga ka7o manas tas gidiza immatha shemposoy awayse gidees” giitte.
Gidan da ya shiga, ku gaya wa maigidan cewa, ‘Malam yana tambaya, ina ɗakin baƙina, inda zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina?’
15 Izikka bolla poqe bolla diza gigi utida aaho so intena bessana, hen izan gigisitte.”
Zai nuna muku wani babban ɗakin sama da aka shirya domin baƙi. Ku yi mana shirin a can.”
16 Iza kalizaytikka kezidi gede katama bida. Wurikka Yesusay gida mala gidi beetides, pazigakka hen gigisida.
Almajiran suka tafi, suka shiga cikin birnin, suka kuwa tarar da kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
17 Gadey qamishin Yesusay bena kaiza tammane namm7atara gakidees.
Da yamma ta yi, sai Yesu ya zo tare da Sha Biyun.
18 Issti madan dishin ta intess tummu gays inte gidoppe issay izikka tanara issippe mizaysi tana athi immana” gidees.
Yayinda suke cin abinci a tebur, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗaya daga cikinku zai bashe ni, wani wanda yake ci tare da ni.”
19 Istika muzotidi “Tanesha? tanesha? gidi issay issay Yesusa” ooychida.
Suka cika da baƙin ciki, da ɗaya-ɗaya suka ce masa, “Tabbatacce, ba ni ba ne, ko?”
20 Izikka istas “Tamane namm7atappe issay tanara ba kushe keren yedizadekko.
Ya ce, “Ɗaya daga cikin Sha Biyun ne, wanda yake ci tare da ni a kwano.
21 Kasse xafetida mala asa nay iza gish hayqana shin asa na athi immizades aye! He uray kasse yeletonta agidakko izas lo7okoshin!” gides.
Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda yake a rubuce game da shi, amma kaiton mutumin da ya bashe Ɗan Mutum! Zai fi masa, da ba a haife shi ba.”
22 Issti mishin uketha eeki anjidinne menthidi bena kalizaytas hayssa ta asho heyte gi imidees.
Yayinda suke cin abinci, sai Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya, ya ba wa almajiransa, yana cewa, “Ku karɓa, wannan jikina ne.”
23 Ushakka denthi galatidi istas imin isti wurikka uyida.
Sai kuma ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, ya kuma miƙa musu, dukansu suka sha daga ciki.
24 Qasse “Haysi darotta gish gukkana ta ooratha caqo suutha.
Sai ya ce musu, “Wannan jinina ne na alkawari, wanda aka zubar da shi saboda mutane da yawa.
25 Ta intes tummu gays ooratha woyneppe gigida usha Xoossa kawotethan ta uyana galasiyo gakanas namm7antho hayssa uyikke.” gides.
Gaskiya nake gaya muku, ‘Ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai ranan nan, da zan sha shi sabo a mulkin Allah.’”
26 Hessafe guye mazmure issippe yexidi pude Dabirazaytte zumma bolla kezida.
Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
27 Yesusay “Ta hemizaysa shocana he wode iza dorssati laletna geteti xafetidaysa mala inte wurikka tanan duphistana.
Yesu ya ce musu, “Dukanku za ku ja da baya ku bar ni, gama yana a rubuce cewa, “‘Zan bugi makiyayin tumaki, tumakin kuwa za su warwatse.’
28 Ta dendidaysappe guye gidikko ta inteppe kasistada Galila bana.” gides.
Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
29 Phixirosaykka “asay wuri dhuphetikkokka tani dhuphetikke!” gides.
Bitrus ya ce, “Ko da duka sun ja da baya suka bar ka, ba zan bar ka ba.”
30 Yesusaykka “Ta ness tumu gays hach qama kutoy namm7u to wasana gakanas neni tana heedzdzu to kadana” gidees.
Yesu ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, yau, tabbatacce, a daren nan, kafin zakara yă yi cara sau biyukai da kanka za ka yi mūsun sanina sau uku.”
31 Phixirosay qass “ta nenara hayqizakkokka mulekka nena kadikke” gidi kehi minthi yotidees. Hankoytikka wuri izaysatho gida.
Amma Bitrus ya yi ta nanatawa da ƙarfi ya ce, “Ko da zan mutu tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Duk sauran ma suka ce haka.
32 Hessappe guye Getesemane getetizaso bida Yesusaykka bena kalizayta “Tanni wosishin inte hayssan gamm7isitte” gidees.
Suka tafi wani wurin da ake kira Getsemane, Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Ku zauna a nan, yayinda ni kuwa in yi addu’a.”
33 Phixirosa, Yaqobene Yanisa benara eeki bidees. Kehi muzotideesne hirgidees.
Ya tafi tare da Bitrus, Yaƙub da kuma Yohanna. Sai ya fara baƙin ciki da damuwa ƙwarai.
34 Qassekka isttas “Ta shempiya daro muzotadus inte han dishittene dhiskonta nagitte” gidees.
Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har ma kamar zan mutu. Ku dakata a nan ku yi tsaro.”
35 Istta achappe guthu gede paqidi biitta bolla gufanidi hanikko he sateya izappe adhana mala wosidees.
Sai ya yi gaba kaɗan, ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a, ya ce in mai yiwuwa ne, a ɗauke masa wannan sa’a.
36 “Abba aabbo, ness wuri danda7etees, hayssa waye xu7a tappe hasa. Gido attin ne sheneppe atin ta sheney hanoppo” gides.
Ya ce, “Ya Abba, Uba, kome mai yiwuwa ne a gare ka. Ka ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba abin da nake so ba, sai dai abin da kake so.”
37 Izi heppe simi yishin iza kalizayti dhisikidayta beyidees. Phixirsokka “Simona dhiskadi? Haray ato shin issi satekka sura utada nagoy nena xonide?
Sai ya koma wajen almajiransa, ya same su suna barci. Ya ce wa Bitrus, “Siman, kana barci ne? Ka kāsa yin tsaro na sa’a ɗaya?
38 Inte pacen gelonta mala begidi wositene minite. Shempoy gigeti utidees shin ashoy gidikko daburancha.” gides.
Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, domin kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
39 Qassekka bidi koyro wosoysathokka wosides.
Ya sāke komawa, ya maimaita addu’ar da ya yi.
40 Izi namm7antho simi yishin issta ayfen dhiskoy dexxin dhiskidayta demides, shin issti izas ay zaranakonne eribeytena.
Da ya dawo, ya sāke tarar da su suna barci, domin barci ya cika musu ido. Suka rasa abin da za su ce masa.
41 Hezantho yidi “Ha7ikka inte zin7idi shempeti? Ha7i gidana, sateyakka gakkadus hekko asa nay nagaranchata kushen adhi immistana.
Da ya koma sau na uku, sai ya ce musu, “Har yanzu kuna barci, kuna hutawa ba? Ya isa! Lokaci ya yi. Duba an ba da Ɗan Mutum a hannun masu zunubi.
42 Ane eqitte boss, tana athi immandey yidees.” gides.
Ku tashi! Mu tafi! Ga mai bashe ni ɗin yana zuwa!”
43 Izi buro hasa7an dishin tamane namm7atappe issay Yuday yidees. Izara issippe qesse halaqatapene Muse woga tamarsizaytappe kitetida daro asay githa mashanne durqa oykidi yidees.
Yana cikin magana ke nan, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun ya bayyana. Ya zo tare da taro da suke riƙe da takuba da sanduna. Manyan firistoci da malaman dokoki, da kuma dattawa ne suka turo taron.
44 Iza athi immana Yuday istas “asa gidoppe ta yerizadey iza gidida gishas oykidi lo7ethi nagi efiite” gidi kaseti malata immi wothides.
Mai bashe shi ɗin ya riga ya shirya alama da su cewa, “Wanda na yi wa sumba, shi ne mutumin, ku kama shi, ku riƙe sosai.”
45 Gakida malara Yuday Yesusakko shiqidi “Astamare” gidi yeridees.
Nan da nan Yahuda ya je wurin Yesu ya ce, “Rabbi!” Ya kuma yi masa sumba.
46 Assatikka Yesusa oykida.
Mutanen kuwa suka kama Yesu, suka riƙe shi.
47 Iza achan eqida issay masha shohoppe shodidi qessista halaqa ashkara hayth qanxidees.
Sai wani cikin waɗanda suke tsattsaye kusa ya zāre takobinsa, ya sare kunnen bawan babban firist.
48 Yesusaykka istas “Panga mala tana oykkana mashane durqa oykidi yeti?
Yesu ya ce, “Ina jagoran wani tawaye ne da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni?
49 Wontin wontin maqidassen tamarsashe ta intenara dishin oykibeykista shin kasse xafetidaysi polistan mala haysi hanidees.” gides.
Kowace rana ina tare da ku, ina koyarwa a filin haikali, ba ku kama ni ba. Amma dole a cika Nassi.”
50 Hessa wode iza kalizayti wuri iza yegi agi bida.
Sai kowa ya yashe shi ya gudu.
51 Be kaloteth qeeri naxalan kamida issi nay Yesusa kalishin asssay iza oykin
Wani saurayin da ba ya sanye da kome sai rigar lilin, yana bin Yesu. Da suka yi ƙoƙarin kama shi,
52 nazi naxala yegidi kallo kichidees.
sai ya gudu ya bar rigarsa, ya gudu tsirara.
53 Yesusakka gede qessista halaqakko efida. Qessista halaqati dere cimatine Muse woga tamarsizayti hen issippe wuri shiqida.
Suka kai Yesu wajen babban firist, sai dukan manyan firistoci, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru.
54 Phixirosaykka Yesusa hahora kalishe qessista halaqa gibe gakanas bidees. Izi hen utidi hara asatara tamma ho7ishin
Bitrus ya bi shi daga nesa, har cikin filin gidan babban firist. A can, ya zauna tare da masu gadi, yana jin ɗumin wuta.
55 qessista halaqatinne dere cimmati wuri Yesusa wodhanas markatana ass koyida shin demanas danda7ibeytena.
Manyan firistoci da dukan’yan Majalisa, suka shiga neman shaidar laifin da za a tabbatar a kan Yesu, domin su kashe shi. Amma ba su sami ko ɗaya ba.
56 Daroti iza bolla wordora markatikkokka markata qalay oyketibeynna.
Da yawa suka ba da shaidar ƙarya a kansa, amma shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
57 Issi issi markati;
Sai waɗansu suka miƙe tsaye, suka ba da wannan shaida ƙarya a kansa, suka ce,
58 “Haysi adezi (Ta asa kushen kexetida maqidasse lalada asa kushey bochontaz hara maqidasse heedzdzu galasara ta kexana) gishin nu siyidos” gi markatida.
“Mun ji shi ya ce, ‘Zan rushe wannan haikali da mutum ya gina, cikin kwana uku, in sāke gina wani wanda ba ginin mutum ba.’”
59 Gidikokka ista markatethi issi bolla woodhibeyna.
Duk da haka ma, shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
60 Qessista halaqaykka ista sinthan dendidi eqqi “Hayti ne bolla markatizaysi aze? Ne aazas duuna zariki?” gidi Yesusa oychidees.
Sai babban firist ya tashi a gabansu, ya tambayi Yesu ya ce, “Ba za ka amsa ba? Wane shaida ke nan waɗannan mutane suke kawowa a kanka?”
61 Gido atin Yesusay isstas aykokka zaronta coo7u gidees. Qessista halaqay qassekka “Anjetida Xoossa nay kirstosay nene?” gi oychidees.
Amma Yesu ya yi shiru, bai kuwa amsa ba. Babban firist ya sāke tambayarsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Mai Albarka?”
62 Yesusaykka zaridi “Ee tanank, asa nay woqama Xoossa ushachana utishininne salo sharara yishin inte iza beyana” gides.
Yesu ya ce, “Ni ne. Za ku kuwa ga Ɗan Mutum yana zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a cikin gizagizan sama.”
63 Qessista halaqay ba mayo dakidi “Nuss hara aza marka koshize?
Babban firist ya yage tufafinsa, ya yi ce, “Ina dalilin neman waɗansu shaidu kuma?
64 Izi casha qaala Xoossa bolla hasa7ishin inte siyidista ha7ich intes ay milatizee?” gides. Istika izas hayqoy beses giidi wurikka issi qalan pirdida.
Kun dai ji saɓon. Me kuka gani?” Duka suka yanke masa hukuncin kisa.
65 Hessa wode issi issi asati iza bolla cuchu cutida, iza ayfe goozi oykidi icishe “anne buro hananaysa yoota” gida. Bagayti qasse shagalan baqishe efida.
Sai waɗansu suka fara tattofa masa miyau, suka rufe masa idanu, suka bubbuge shi da hannuwansu, suka ce, “Yi annabci!” Masu gadin kuma suka ɗauke shi, suka yi masa duka.
66 Phixirosay duge bagara hen gibbe gidon dishin qesista halaqa garadistappe issiniya yadaus.
Yayinda Bitrus yake ƙasa a filin gidan, sai wata yarinya, baiwa, ɗaya daga cikin ma’aikatan babban firist, ta zo can.
67 Phixirosay tama ho7ishin tish hista xeladane “Neni Nazirete Yesusara dasa gidikki?” gadus.
Da ta ga Bitrus yana jin ɗumi, sai ta dube shi da kyau. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu, Banazare.”
68 Izi qass “Ne gizaysade ta erikke, ne gizays tass gelena” gidi kadidees. Hessafe gede penge poqi eeqi dishin herakka kutoy wasidees.
Amma ya yi mūsu ya ce, “Ban san abin da kike magana ba, balle ma in fahimce ki.” Sai ya fita zuwa zaure.
69 He garadeya iza be7idamala hen eeqida asatas “Haysi adezi izara diza asatappe issadekko!” gada qassekka hasa7adus.
Da baiwar ta gan shi a can, sai ta sāke gaya wa waɗanda suke tsattsaye a wurin, ta ce, “Wannan mutum yana ɗaya daga cikinsu.”
70 Izi qassekka kadides. Gutha wode gamm7ishin hen eqida asati Phixirossa “Neni Galila asa, hessa gish tummappe ne isstappe issade” gida.
Sai ya sāke yin musu. Bayan ɗan lokaci kaɗan, sai waɗanda suke tsattsaye kusa suka ce wa Bitrus, “Lalle, kana ɗaya daga cikinsu, gama kai mutumin Galili ne.”
71 Gido atin izi qass “inte gizade ta erikke” gishe caqonne bena qangeth oykidees.
Sai ya fara la’antar kansa, yana rantsuwa musu, yana cewa, “Ban san wannan mutumin da kuke magana a kai ba.”
72 Herakka kutoy namm7antho wasidees. Phixirosaykka “kutoy namm7a wasanas ne tana hedza kadana” gida Yesusa qalay izas qopetin hiqumidi yekides.
Nan da nan zakara ya yi cara sau na biyu. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi masa cewa, “Kafin zakara yă yi cara sau biyu, za ka yi mūsun sanina sau uku.” Sai ya fashe da kuka.

< Marqqossa 14 >