< Marqqossa 13 >
1 Izi maqidaseppe kezishin iza kalizaytappe issay astemare haysi kethaynne kethay kexetida shuchay ay mala lo7izakkone hayssa beyay? gidees.
da Yesu ke fita daga Haikalin, sai daya daga cikin almajirnsa ya ce masa “malam, dubi kyawawan duwatsunnan da kyawawan gine-ginnenan!”
2 Yeusayakka zaridi “hayta giitta kethata xelay? shucahti issay issa bolla diza mala detena, wurikka lalistana” gidees.
Ya ce masa, ka ga wadannan kyawawan gine- ginen? babu wani dutsen da za a bar shi akan dan'uwansa, da ba za a rushe shi ba.”
3 Yeususay maqidaseza ginara Dabirazayte zumma bolla utidishin Phixirosay, Yaqobey, Yanisaynne Indirasay xalla izakko shiqidi
Yana zaune a kan dutsen zaitun wanda yake kusa da Haikali, sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawus suka tambaye shi a asirce, suka ce.
4 “Haysi ayde hananakkone nus yot. Haysi wursethan polistanas malatay aze? gi oychida.
Gaya mana yaushe za a yi wadannan abubuwa? mecece zata zama alamar faruwar wadanna abubuwa da zasu faru?''
5 Yesusaykka istas hizgidees “Oonikka intena balethonta mala nagetite.
Yesu ya ce masu, “ku kula, kada kowa ya rudeku.
6 Buro daroti (Ta Kirstosa) gishe ta sunthan yana, darotakka balethana.
Da yawa za su zo da sunana, suna cewa nine shi, har su bad da mutane da yawa.
7 Inte olanne olla wore siyiza wode dagamopitte. Hessi hananaysi attena. wursethi gidikko burona.
In kuka ji labarin yake- yake, da jita-jitarsu kada ku damu, wannan zai faru, amma karshen duniya bai gabato ba.
8 Derey dere bolla kawoy kawo bolla dendana, daroson bitta qathinne qoshay hanana, heyti wuri mixas leeso malla.
Al'umma za ta tasarwa al'umma, mulki ya tasarwa mulki. Za a yi girgizar kasa awurare dabam-dabam, da kuma yunwa, amma fa dukkan wadanna abubuwan mafarin azaba ne.
9 Inte intes nagetite. Buro intena dere dulatan athi immana. Isti intena Ayhudata wossa kethan garafana. Inte ta markata gidana mala ta gish dere dananata sinthaninne kawota sinthan eeqana.
Amma, ku zauna a fadake. Don za su kai ku gaban majalisa. za a yi maku duka a cikin majami'u. Su kuma kai ku gaban masu mulki da sarakuna, saboda sunana, domin ku ba da shaida a gare su.
10 Kyoyrotidi mishiracho qalay dere wursos sabakistana beses.
Amma lallai sai an fara yi wa dukkan al, ummai bishara.
11 Inte oyketidi pirdas shiqiza wode hino he sateyin intes immetizaro hasa7ite atin bidi nu ay gino gidi kaseti hirgopitte. Hasa7anay Xiillo Ayanappe atin intena gideketta.
Sa'ad da suka kai ku gaban shari'a suka mika ku, kada ku damu a wannan lokacin, za a baku abin da zaku fada, Amma duk abin da aka yi muku a wannn lokacin, shi za ku fada, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu mai tsarki ne.
12 Ishay isha aaway ba na hayqos athi immana. Nayti bena yelidayta bolla makal7ananne wodhana.
Dan'uwa zai bada dan'uwarsa akashe shi, uba kuwa dansa. Yara kuma zasu tayar wa iyayensu har su sa akashe su.
13 Ta gedon inte asa wurson ixetidayta gidana. Wurseth gakanas mini eeqidadey gidikko atana.”
Za a ki ku saboda sunana, amma duk wanda ya jumre har karshe zai cetu.
14 Inte, dhaysana tunatethi izas besontason eeqidashe beykko nababizadey wozinan wotho, Yudan dizayti pude zumma bolla gangeto.
Sa'adda kuka ga an kafa mummunan aikin sabo mai ban kyama a wurin da bai kamata ba (bari mai karatu ya fahimta), to, bari wadanda suke kasar Yahudiya, su gudu zuwa dutse.
15 Ketha karen dizadey so gelofo ba miish kesana gidi kethe geloppo.
Wanda yake tudu kuma kada ya sauko ya shiga gida garin daukar wani abu.
16 Goshason dizadey ba mayo ekanas guye simoppo.
Wanda yake gona kuma kada ya koma garin daukar mayafinsa.
17 He galasatan qanthera diza macashatasine na dhanthizaytas aye ana!
Amma, kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokacin.
18 Hessikka balgon gidonta mala Xoossu wositte.
Ku yi addu, a kada abin ya faru da damina.
19 Koyro Xoossi medhetetha wursi medhosoppe ha7i gakanas woykko hayssappe guye izara lemusotizay baynda gitta metoy hanana.
A lokacin za ayi wata matsanaciyar wahala, wadda bata taba faruwa ba, tun farkon halittar da Allah ya yi har zuwa yau, ba kuwa za a taba yi ba har abada.
20 Goday he galasata qanthotakkao oonikka atena shin bess doretidayta gish he galasata qanthides.
In da ba ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba Dan adam din zai tsira. Amma saboda zabbabunan da ya zaba, ya rage kwanakin.
21 He wode oonikka hekko kirstosay hayssan dees, gikko woykko hekko hen dees gikko amanopitte.
To, in wani ya ce maku, kun ga Almasihu nan!' ko, 'kun gan shi can, kada ku gaskata.
22 Wordo kirstosatinne wordo nabeti buro dendidi malatatane kasse hani eeronta palamish oothon istas danda7etikko haray ato shin doretidaytakka balethana.
Gama almasihan karya, da annabawan karya zasu bayyana kuma, zasu yi abubuwan al'ajibai masu ban mamaki.
23 Hessa gish nagetite, he wodey gakonta dishin haara hayssa ubbaa ta intes yotadis.
Amma ku zauna a fadake, Na dai fada maku wadannan abubuwan kafin lokacin.
24 He wode he metozappe kalidi awa arshey dhummana aginaykka po7uku.
Amma, bayan matsanaciyar wahalannan, rana zata duhunta, wata kuma ba zai bada haske ba.
25 Xoolinteti saloppe qoqofistana, salon diza wolaqamati qaaxana.
Taurari za su fado daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.
26 He wode asa nay gitta wolqarane bonchora salo sharara yishin asay iza beyana.
Sa' annan zasu ga Dan mutum na zuwa a cikin gajimare, da iko mai girma da daukaka.
27 Izikka kiitanchata yedidi oydu bagafe/mizaneppe/ biitta gaxappe salo gaxa gakanas diza bess doretidayta shishana.
Zai aiko da mala'ikunsa su tattaro zabbabunsa daga kusuwoyi hudu na duniya(watau Gabas da Yamma, kudu da Arewa) har zuwa karshen sama.
28 Lumusoza balase miththafe tamaritte. Unquloy cililiza wode haythe kesishin bonney matidaysa inte ereista.
“Ku yi koyi da itacen baure. Da zarar rassansa sun fara taushi yana kuma fitar da toho, kun san damina ta yi kusa ke nan.
29 Hesathokka hayti ta gidayti poletishin inte beykko wodey mati yidi penge gakidayssa erite.
Sa'adda kuka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku dai sani ya kusato, a bakin kofa ma ya ke.
30 Ta intes tumu gays ha yoti polistana gakanas haysi ha yeletay adhena.
Hakika ina gaya maku, zamanin nan ba zai shude ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
31 Saloynne haysi biittay adhana shin ta qalay gidikko adhena.
Sararin sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
32 Qasse he glasay gish woykko he satey gish ta aawappe atin salo kitanchata gidinkka naza gidnkka onikka erena.
Amma wannan rana ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai dai Uban kadai.
33 Hessa gish wodey aydekkone inte eronta gish nagetite, minitene wositte.
Ku kula, ku zauna a fadake, kuna addu'a don baku san ranar da lokacin zai yi ba.
34 Haysikka ba keth ashikaratas agidi; ashskarata issa issa iza iza ootho oythidi penge nagizaysi begidi nagana mala azazidi bida asa milates.
Kamar yadda mutum mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta bayinsa kan gidansa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai gadi ya zauna a fadake.
35 Histikko ketha aaway wode yanakone woykko qama gidi gidoth yanakone woykko kutoy wasishin yanakone woykko wonta bolla sosey zo7ishin yanakko inte erontagish begidi nagitte.
To, ku zauna a fadake don ba ku san lokacin da maigidan zai zo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne.
36 Izi yishin inte qopponta zin7idashe izi intena demofo.
Kada ya zo ba zato, ya samu kuna barci.
37 Ta intes yotizaysa asa wursos yotays, minidi nagite) gays.”
Abinda na gaya maku, ina gaya wa kowa, shine ku zauna a fadake!”