< Luqaassa 14 >

1 Issi gallas Yesussay quma maanaas Farsawista halaqatape issa so gelida wode asay wuri Yesussa ay oothanakonne gidi ayfe iza bolla tooki xellides.
Wata ranar Asabbaci, da Yesu ya shiga gidan wani sanannen Bafarisiye don cin abinci, sai mutane suka zuba masa ido da kyau.
2 Heenka asatethay izas purin wayetiza issi assi iza sinthan dees.
A nan a gabansa kuwa akwai wani mutum mai ciwon kumburin ƙafa da hannu.
3 Yesussaykka Muse woga erizaytanne Farsawista saketizadde sanbbata gallas pathanaas koshize koshennee? gidi oychchides.
Sai Yesu ya tambayi masanan dokoki da Farisiyawa ya ce, “Daidai ne bisa ga doka, a yi warkarwa a ranar Asabbaci, ko babu?”
4 Istika co7u gida izikka addezza bochchiddi pathi yeddides.
Amma ba su ce kome ba. Sai ya riƙe mutumin, ya warkar da shi, sa’an nan ya sallame shi.
5 Qassekka intefe issi asas sanbbata wode nay woykko booray kundidi olan geliko eeson heeraka kesonta uray oone? gides.
Sai ya tambaye, su ya ce, “In wani a cikinku yana da ɗa, ko bijimi da ya faɗa a rijiya a ranar Asabbaci, ba za ku cire shi nan da nan ba?”
6 Istika oychas aykko zaroka demmnaas dand7ibeyitenna
Suka rasa abin faɗi.
7 Xeygetida asati uttanaas boncho so koyishin Yesussay beyidi leemuso istas hiz gidi yoottides.
Da ya lura da yadda baƙi suna zaɓan wuraren zama masu bangirma a tebur, sai ya faɗa musu wannan misali, ya ce;
8 Issi assi nena sarges xeysiko boncho son utofa, nepe bollara bonchetizaddey xeysetiko
“In wani ya gayyace ka bikin aure, kada ka zaɓi wurin zama mai bangirma, don wataƙila akwai wani da ya fi ka girma, da aka gayyata.
9 Intena nam77antaka xeysidaddey yiidi ne utidasoza hayssaddes yeda gaana, nenika yelatashe ziqaso banddassa.
In kuwa haka ne, wanda ya gayyace duk biyunku, zai zo ya ce maka, ‘Ka ba wa mutumin nan wurin zamanka.’ Ka ga, an ƙasƙantar da kai, kuma dole ka ɗauki wuri mafi ƙasƙanci.
10 Gido attin xeysetida wode ziqaso xellada utta, nena xegidaddey yiidi ta lagge haaya dhoqason utta gaandes, nenika he wode nenara maaddan utida asa wurso sinthan bonchetana.
Amma in an gayyace ka, ɗauki wuri mafi ƙasƙanci, don in wanda ya gayyace ka ya zo, zai ce maka, ‘Ka hawo nan aboki a wuri mafi girma.’ Wannan zai ɗaukaka ka a gaban dukan’yan’uwanka baƙi.
11 Ays giiko bena dhoqqu histizaddey wuri ziq gaana bena ziq histizaddey wuri dhoqqu gaana.
Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Shi wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
12 Yesussaykka xeygidaddeza hiz gides quma woykko ka7o muzanas xeysiko neysatho nena xeysidi muzonta mala ne laggeta woykko ne ishata, ne dabota, woykko durista woykko dure guttata xegopa
Sai Yesu ya ce wa wanda ya gayyace shi, “Lokacin da ka shirya biki ko liyafa, kada ka gayyaci abokanka, ko’yan’uwanka, ko danginka, ko kuma maƙwabtanka masu arziki, gama in ka yi haka, suna iya gayyatarka, su biya maka alherin da ka yi musu.
13 Gido attin asa xeysada muzana koyko manqota, kushey toy bayndda wobistane qooqeta xeysa neni anjetana.
Amma lokacin da ka kira biki, ka gayyaci matalauta, da guragu, da shanyayyu, da makafi.
14 Xeysetidayti kushe zaranaas danda7onta gish xillota dentha wode nees kushey zaretana.
Ta haka, za ka sami albarka. Ko da yake ba za su iya biyan ka ba, za a biya ka a ranar tashin masu adalci daga matattu.”
15 Maaddan Yesussara issife utidaytape issay hayssa siyidi Xoossa kawotethan shiiqidi maaddafe miza uray anjetidadde gides.
Da jin haka, sai wani da yake tare da shi a tebur ɗin, ya ce wa Yesu, “Mai albarka ne wanda zai ci abinci a bikin nan a mulkin Allah.”
16 Yesussaykka hizgides issi assi wolqama diggisa giigisidi daro assi xeygides.
Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum yana shirya wani babban biki, ya kuma gayyaci baƙi da yawa.
17 Diggissa maana wodeyka gakin xeygetida imathata wurikka giigida gish ha yite gidi xegana mala ba ashkkara yeddides.
Da lokacin bikin ya yi, sai ya aiki bawansa ya je ya ce wa waɗanda aka gayyata, ‘Ku zo, don an shirya kome.’
18 Gido attin wurikka beso hara gaaso shiishidi isoy ha7i gade shamadis baada beyanas besses hachsi tana lancofa gides.
“Amma sai dukansu suka fara ba da hujjoji. Na farkon ya ce, ‘Na sayi gona yanzun nan, dole in je in ga yadda take, ina roƙonka ka yi mini haƙuri.’
19 Hankoysika tani ichachu waxa boora shamadis izista paaca xellana gish hach tana lancofa gides.
“Wani ya ce, ‘Na sayi shanun noma guda goma yanzun nan, ina kan hanyata ke nan in gwada su, ina roƙonka, ka yi mini haƙuri.’
20 Qasse hara asaykka tani buro miishratethan days baannaas danda7ikke gides.
“Har yanzu wani ya ce, ‘Na yi aure yanzun nan, don haka ni ba zan iya zuwa ba.’
21 Oothanchayka kitetida soope simmidi hezati gidayssa ba Godas yoottides. he wodeka diggisa giigisidays hanqetidi oothancha hizgides, elella oydu oge kezada manqota, kusheynne toy bayndda wobista qomaxatanne ayfey bayndda qooqeta ha geltha gides.
“Bawansa ya dawo ya gaya wa maigidansa wannan. Sai maigidan ya yi fushi, ya ba da umarni ga bawansa ya ce, ‘Ka fita da sauri, ka bi titi-titi da lungu-lungu na garin, ka kawo matalauta, da guragu, da makafi, da shanyayyu.’
22 Oothanchayka zaaridi ta Godo ne tana azazidaysa wursa poladis burokka utetha soy dees gides.
“Bawan ya dawo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, an yi abin da ka umarta, amma har yanzu da sauran wuri.’
23 Godazikka oothanchaza gede oydu oge keza ta keeth kumana mala pudene dugenne aadhdhizaytta wolqara geltha.
“Maigidan ya ce wa bawansa, ‘Ka je kan hanyoyin da layi-layi na karkara, ka sa su shigo, don gidana ya cika.’
24 Tani tuma gays diggisa maana xeysetidaytape issi urayka duunan gelthenna gides.
Ina gaya muku, babu ko ɗaya daga cikin mutanen nan da aka gayyata da zai ɗanɗana bikina.”
25 Daro derey izara issife bizayssa beyidi guye simmida Yesussay hizgides.
Taron mutane mai yawa suna tafiya tare da Yesu, sai ya juya ya ce musu,
26 Taako yizay wuri ba aawanne ba, ba machchonne nayta, ba ishatanne michchista ba duus gidiin ixonta agikko tana kaallizadde gidanas danda7enna.
“Duk wanda yakan zo wurina, amma bai ƙi mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa da’ya’yansa, da’yan’uwansa mata da maza, kai, har ma ransa ba, ba zai iya zama almajirina ba.
27 Be masqale tookidi tana kaalontay tana kaallizadde gidanas danda7enna.
Kuma duk wanda ba yakan ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
28 Inte issi assi keethe keexanas koyko polanaas danda7anakkonne danda7ontako koyrotidi ba bira qopontay oone?
“In wani daga cikinku yana so ya gina gidan sama, ai, yakan fara zama ne, ya yi lissafin abin da ginin zai ci tukuna, don yă ga ko yana da isashen kuɗi da zai gama ginin.
29 Keetha keexana doomidi wursanaas hanonta ixxiko beydda assi wuri iza bolla miicana.
Gama in ya sa tushen gini, amma bai iya gamawa ba, duk wanda ya gani zai yi masa ba’a,
30 Istika hizgana haysi addezzi keeth oykides shin polibeyna.
yana cewa, ‘Wannan mutum ya fara gini, amma bai iya gamawa ba.’
31 Woykko issi kawoy hara kawora olistana giigiidi nam77u tamu shi asa assi ekki yiza kawo zaranaas tamu shi ola asara zaranakonne uttidi qopontay oone?
“Ko kuma, wane sarki ne, in zai je yaƙi da wani sarki, ai, yakan fara zama ne, ya duba ya ga, ko da mutane dubu goma, shi zai iya ƙarawa da mai zuwa da dubu ashirin?
32 Ola zaranaas danda7ettontta milatida bettikko buro hahon dishin maqaynanas gaana yedes.
In ba zai iya ba, to, tun suna nesa, zai aika da wakilai, su je neman sharuɗan salama.
33 Izaka mala inte oonikka gidiin bees dizaysa aggontay oonikka tana kaallizadde gidanas danda7enna.
Haka nan fa, kowane ne a cikinku, da ba ya rabu da abin da yake da shi ba, ba zai iya zama almajirina ba.
34 Maxiney lo7oshin maxiney mal7onta ixxiko go7ena,
“Gishiri fa yana da kyau, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa?
35 Gadeni yegin gidonta gish co kare wora yegetes siyiza haythi diza assi siyo.
Ba shi da wani amfani, ko ga ƙasa, ko ga juji, sai dai a zubar da shi. “Duk mai kunnen ji, yă ji.”

< Luqaassa 14 >