< Yaqobeppe 1 >
1 Xoossa Goda Yesusi Kiristossa oothancha gidida Yaqobeppe biitta bolla laletida tammane nam77u kochatas sarotethi intes gido.
Yaƙub, bawan Allah da kuma na Ubangiji Yesu Kiristi, Zuwa ga kabilan nan goma sha biyu, da suke warwartse a cikin al’ummai. Gaisuwa mai yawa.
2 Ta ishato inte bolla duma duma wayey gakkiiko hessa wursi ufaysan qoodite.
Ku ɗauki wannan da farin ciki mai tsabta,’yan’uwana, duk sa’ad da gwaje-gwaje na kowane iri suka zo muku,
3 Gaasoykka inte amano paccetithi intes danda7a immizayssa inte ereetta.
domin kun san cewa gwajin bangaskiyarku yakan haifi daurewa.
4 Inte danda7an mini eqanaysi intes issi miishshikka pacconta kumetha assine wothoy bayndayta gidana mala ootho.
Dole daurewa ta kammala aikinta don ku zama balagaggu da kuma cikakku, ba ku kuma rasa kome ba.
5 Inte garssafe oonasikka eratethi pacciko oonakka kadhontta ba kiiyatethara wurisos immiza Xoossa wosso; izadeskka imettana.
In waninku ya rasa hikima, ya kamata yă roƙi Allah, mai bayarwa hannu sake ga kowa ba tare da gori ba, za a kuwa ba shi.
6 Gido attin sidhey baynda amanon wosso. Gaasoykka sidhiiza uray abba qathiza bullahe cariko malakko.
Amma sa’ad da ya roƙa, dole yă gaskata, ba tare da shakka ba, domin shi mai shakka, yana kama da raƙumar ruwan tekun da iska take kori tana kuma ɓuɓɓugowa.
7 Hessadey Godape aykokk demana giidi issinokka qoppofo.
Kada irin wannan mutum yă yi tsammani zai sami wani abu daga Ubangiji;
8 He uray nam77u qohaaththaan ooyketidi ba bizza oge bolla hene haane giza asa malakko.
shi mai zuciya biyu ne, marar tsai da zuciyarsa wuri ɗaya a cikin duk abin da yake yi.
9 Kase ziiqan diza ura Xoossi dhoqqu histiza gish ufa7etto.
Bari ɗan’uwan da yake cikin halin ƙasƙanci yă yi taƙama a matsayinsa na ɗaukaka.
10 Asa haroy maata cisha mala qoqofettiza gish dure ura Xoossi ziq histikko ufa7etto.
Amma wanda yake mai arziki, ya kamata yă yi taƙama a matsayinsa na ƙasƙanci, gama ba zai daɗe ba kamar furen jeji.
11 Away xugidi maata shullisees; maata ciishayka shullees; iza loo7etethikka dhayees; hessathokka durey hachchi hachchi dabursan diishin iza duretethi dhayees.
Gama in rana ta fito ta yi zafi mai tsanani sai ta sa tsiro yă yanƙwane tsiro; furensa yă kakkaɓe, kyansa kuma yă lalace. Haka ma mai arziki zai shuɗe yayinda yake cikin harkarsa.
12 Paccen miinni eqidadey izi anjjetidade. Gaasoyka izi paccera eqitishin Xoossi bena dosizaytas immida ufaysa deyo zawude izi ekkana.
Mai albarka ne mutumin da yake daurewa cikin gwaji, gama bayan ya yi nasara da gwajin, zai sami rawanin rai wanda Allah ya yi alkawari ga waɗanda suke ƙaunarsa.
13 Oonikka paccetiza gidikko tana Xoossi paccees goppo, gaasoykka Xoossi ase iittan paccena, izi oonakka pacci erena.
Sa’ad da aka jarrabci mutum, kada yă ce, “Allah ne yake jarrabtarsa.” Gama ba ya yiwuwa a jarrabci Allah da mugunta, shi kuma ba ya jarrabtar kowa;
14 Gido attin issi issi uray paccetizay berika ba iitta amo kalishene baletishekko.
amma akan jarrabce kowane mutum sa’ad da muguwar sha’awarsa ta janye shi ta kuma rinjaye shi.
15 Amoy qanthetetidape guye nagara yellees. Nagaraykka dicciidape guye hayqo yellees.
Sa’an nan, bayan da sha’awar ta yi ciki, takan haifi zunubi; zunubi kuwa, sa’ad da ya balaga yakan haifi mutuwa.
16 Ta siiqo ishato inte ballettopite.
Kada a ruɗe ku,’yan’uwana ƙaunatattu.
17 Loo7o imotethine kumetha anjjoy wuri bolla Salo poo7ota Aawape wodhetes. Iza achan gede ha yuyiza kuwayka (eshoykka) dena.
Kowane abu mai kyau da kuma kowace cikakkiyar kyauta daga sama suke, sun sauko ne daga wurin Uban haskoki, wanda ba sauyawa ko wata alamar sākewa a gare shi faufau.
18 Nu iza medhetethas koyro bayrata gidana mala ba sheninne ba tuma qaalan nuna yellides.
Ya zaɓa yă haife mu ta wurin kalmar gaskiya, domin mu zama’ya’yan fari na dukan abin da ya halitta.
19 Dosetida ta ishato hayssa yuushi qoppite. Asi wurikka siyanas esoto, hasa7asinne hanqqos esotopo.
’Yan’uwana ƙaunatattu, ku lura da wannan. Ya kamata kowa yă kasance mai saurin saurara, ba mai saurin magana ba, ba kuma mai saurin fushi ba,
20 Asa hanqqoy Xoossa xiiloteth oothena.
gama fushin mutum ba ya kawo rayuwar adalcin da Allah yake so.
21 Hessa gish tunatethinne dalggida iittatethi intefe kessi yegidi inte shemppo ashanaas danda7iza inte gidon toketida qaala ashketethara ekkite.
Saboda haka, ku rabu da ƙazamin hali da kuma kowace irin mugunta ku kuma yi na’am da maganar da aka shuka a cikinku da tawali’u, wadda za tă iya cetonku.
22 Qaalay gizayssa oothite; attin mela siisi xalala siyzadista gididi interkka intena balethofite.
Kada ku zama masu ji kawai, ku ruɗi kanku. A maimakon haka ku zama masu yin abin da ta ce.
23 Qaala siyishe siyida qaalay gizayssa oothontadey ba ayfeso mastotera xelliza asa malakko.
Duk wanda yake ji magana ne kawai, bai kuwa aikata abin da ta ce ba, yana kama da mutumin da ya kalli fuskarsa a madubi
24 Bena xeelli beydi bees; izi ay milatizakone heraka baletti gides.
bayan ya kalli kansa, sa’ad da ya tashi daga wurin, nan da nan sai yă manta da kamanninsa.
25 Gido attin bena geshiza loo7o woga xeelli beydi izan minizadey ba siydayssa oothizadeynne balonttadey izi ba oothon anjjetidade gidana.
Amma duk mai duba cikakkiyar ƙa’idan nan ta’yanci, ya kuma nace a kanta, ya zama ba mai ji ne kawai yă mance ba, sai dai mai yi ne yă zartar, to wannan shi za a yi wa albarka a cikin abin da yake yi.
26 Be duuna nagontta berikka ba wozina baleththishe ta ammanayss gizadey berikka bena baleththees. Iza ammanoykka mella hada ammanokko.
In wani ya ɗauki kansa mai addini ne duk da haka bai ƙame harshensa ba, ruɗin kansa yake yi addininsa kuwa banza ne.
27 Xoossa Aawa sinthan iittatethi baynda loo7o ammanoy; “Aayanne Aaway hayqqida nayta, istta azinati hayqqida maccashata metotetishin maadonne hayssa alameza tunatethafe bena nagokko.
Addinin da Allah Ubanmu ya yarda da shi a matsayin mai tsabta da kuma marar aibi shi ne, a kula da marayu da gwauraye cikin damuwoyinsu, a kuma kiyaye kai daga lalacin da duniya take sa wa.