< 3 Yanisa 1 >
1 Taape ciimazape, tumape ta siiqiza ta siiqqo laagge gayyosas.
Dattijon nan, Zuwa ga ƙaunataccen abokina Gayus, wanda nake ƙauna ƙwarai da gaske.
2 Ta ishazo, ne shempoy loo7on dizamala ne asatethay loo7o dana malane ne oothizazi wurikka nees giiga gidanamala ta nees wossays.
Abokina ƙaunatacce, ina addu’a ka sami zaman lafiya don kome yă yi maka daidai, kamar yadda ruhunka yake zaune lafiya.
3 Ne tumas amanetidade gidida mala qassekka ne hanoy wuri tumu gididaysa isi isi amaniza asati taakko yidi ne gish yotiin siyada ta daro ufa7istadis.
Na yi farin ciki ƙwarai sa’ad da waɗansu’yan’uwa suka zo suka yi zance game da yadda kake da aminci ga gaskiyan nan da kuma yadda kake cin gaba cikin gaskiyan nan.
4 Gasoykka ta nayti loo7onne tuman smeretishin siisafe adhiza hara ufaysi tas deena.
Ba abin da ya fi sa ni farin ciki fiye da in ji cewa’ya’yana suna cikin gaskiyan nan.
5 Ta ishazo issti nes imath gidikokka nenii ne ishatas oothida mishe wurson amanistadasa.
Abokina ƙaunatacce, kana da aminci cikin abin da kake yi wa’yan’uwa, ko da yake su baƙi ne a gare ka.
6 Ne bolla ay mala siiqqoy dizakone isti ne gish wosa keeththa asa sinthan marikatida. Isti biiza oogen Xooss ufaysiza hanon ne ista madikko loo7o oothassa.
Sun faɗa wa ikkilisiya game da ƙaunarka. Za ka kyauta in ka sallame su a hanyar da ta cancanci Allah.
7 Ays gikko isti Xoossa amanontaytape aykokka ekonta Kirstossa suntha gish mela kezida.
Saboda Sunan nan ne suka fito, ba sa karɓan wani taimako daga waɗanda ba masu bi ba.
8 Hesa giish nu isippe tumas oothan mala heytanta malata mokkii ekana beses.
Saboda haka ya kamata mu nuna halin karɓan baƙi ga irin mutanen nan domin mu yi aiki tare saboda gaskiyan nan.
9 Ta Wossa keethas hayssafe kase xafadis. Gido attiin kallethizade gidana koyiza Diyoxraxossay nu gizaz ekena.
Na rubuta wa ikkilisiya, amma Diyotirefes, wanda yake son zama na farko, ya ƙi yă yi hulɗa da mu.
10 Hesa gish, ta he bikko izi ba ita qalan nu sunthu moranas oothidaysa ta intes qonccisana. Hesikka izas gidonta ixin amaniza asa mokki ekena; Mokkii ekana koyzaytakka digesinne wossa keethafe kesi godes.
Saboda haka in na zo, zan tone abin da yake yi, yana surutu game da mu, yana ɓaɓɓata mu. Wannan ma bai ishe shi ba, har yana ƙin marabtar’yan’uwa. Yana hana waɗanda suke so yin haka, yana ma korinsu daga ikkilisiya.
11 Ta ishazo, loo7ota milata attiin ita asata milatopa. Loo7o oothizadey wurikka Xoossa asa. Ita oothizadey qasse Xooss beybeyna.
Abokina ƙaunatacce, kada ka yi koyi da abin da yake mugu sai dai abin da yake nagari. Duk mai yin abin da yake nagari daga Allah yake. Duk mai yin abin da yake mugu bai taɓa sanin Allah ba.
12 Dimexrosas asi wuri loo7o markates. Tumaykka izas markataysu. Nukka izas markatos, intekka nu markkay tumu gididaysa ereta.
Demetiriyus yana da shaida mai kyau daga wurin kowa, har gaskiya kanta ma ta shaide shi. Mu ma muna ba da shaida mai kyau a kansa, ka kuma san cewa shaidarmu gaskiya ce.
13 Ta nees xahaaththaana buro daro yoy dees shin ta nes waraqatan xahaaththaanas koyikke.
Ina da abubuwa da dama da zan rubuta maka, sai dai ba na so in yi amfani da alƙalami da inki in rubuta su.
14 Ta nena mata wode beyanas ufays oothays, he wode nu isife uti hasa7ana. Ane saron da; ne lageti nena saro saro getes, ta lagista sunthu sunthu xeygada saro ga.
Ina fata in gan ka nan ba da daɗewa ba, za mu kuwa yi magana fuska da fuska. Salama gare ka. Abokai a nan suna gaishe ka. Ka gai da abokai a can da sunansu.