< 1 Yanisa 1 >

1 Dey qaala gish koyrope dizayssa nu nu haythan siydaysane nu ayfera be7idaysa loo7ethi xellidays nu kushera ooyki be7idassa gish hsa7os.
Wannan da ya kasance tun farko, wanda muka ji, wanda muka gani da idanunmu, wanda muka duba, hannuwanmu kuma suka taɓa, wannan ne muke shela game da Kalman rai.
2 Deyoykka qoncides, nukka nu ayfera beydi markatos. Izas iza aawa achan dizasane nuskka qoncida medhiina deyo gish nu intes Yootos. (aiōnios g166)
Wannan Rai ya bayyana, muka kuwa gan shi, muka kuma shaida shi, muna kuwa yin muku shelar wannan rai madawwami, wanda dā yake tare da Uba, ya kuma bayyana a gare mu. (aiōnios g166)
3 Inteskka nunara isipetethi dana mala nuni be7idaysanne siydaysa intes yootos. Nu isipetethayka aawarane iza na Yesus Kiristossarako.
Muna yin muku shelar abin da muka gani, muka kuma ji ne, domin ku ma ku yi zumunci tare da mu. Zumuncinmu kuwa yana tare da Uba da kuma Ɗansa, Yesu Kiristi.
4 Nu ufaysay kumetha gidanamala nu hayssa intes xafosu.
Muna rubuta wannan domin farin cikinmu yă zama cikakke.
5 Nu izape siydi intes yootiza kiitay Xoossi poo7o iza acahan mulekka dhumay dena gizaysako.
Wannan shi ne saƙon da muka ji daga wurinsa, muna kuma sanar da ku cewa Allah haske ne; a cikinsa kuwa babu duhu ko kaɗan.
6 Nu dhuman simeretishe izara nuusu isipetethi dees; Nu giiko wordotosu attin tuman dokko.
In muka ce muna zumunci da shi amma muna tafiya cikin duhu, ƙarya muke yi, kuma ba ma rayuwa bisa ga gaskiya.
7 Gido attin izi poo7on diza mala nukka poo7on simeretiko nu garisan nuus isipetethi dees; iza na Yesuss Kirstosa suthi nuna Nagara wurisofe geshees.
Amma in muna tafiya cikin haske, yadda yake cikin haske, muna da zumunci da juna ke nan, kuma jinin Yesu, Ɗansa, yana tsarkake mu daga dukan zunubi.
8 Nu nunan nagaray bawaa gikko nurka nuna balethos; Tumaykka nunan deena.
In muka ce ba mu da zunubi, muna ruɗin kanmu ne, gaskiya kuwa ba ta cikinmu.
9 Nuni nu nagara paaxiiko izi nu nagara atto ganasinne nu marika7atethafe nuna wursi geshanas izi amanetidadene xiiloko.
In muka furta zunubanmu, shi mai aminci ne, mai adalci kuma, zai gafarta mana zunubanmu, yă kuma tsarkake mu daga dukan rashin adalci.
10 Nu nagara oothi beyko giikko iza nu woradancha kesosne iza qalayka nunan dena.
In muka ce ba mu yi zunubi ba, mun mai da shi maƙaryaci ke nan, maganarsa kuwa ba ta da wuri a cikinmu.

< 1 Yanisa 1 >