< 1 Yanisa 2 >
1 Ta nayto ta intes hayssa xafizay inte nagara oothonta malako gido attin oonikka nagara oothiko Aawa achan nus xabaqay dees. izika xiilloza Yesuss Kirstossako.
’Ya’yana ƙaunatattu, ina rubuta muku wannan ne don kada ku yi zunubi. Amma in wani ya yi zunubi, muna da wani wanda yake magana da Uba don taimakonmu, wato, Yesu Kiristi, Mai Adalci.
2 Izi nu nagaray atto geetetena mala oge gigisizade. Hesikka nuna xalala gidontta kumetha alame asasara attin nuus xalla gidena.
Shi ne hadayar kafara saboda zunubanmu, kuma ba don namu kaɗai ba amma har ma da zunuban duniya duka.
3 Nu iza azazota polliko nu iza eridaysa hessan amanetos.
Ta haka za mu tabbata cewa mun san shi in muna yin biyayya da umarnansa.
4 “Ta iza erays” Gishe iza azazo polontade gidiko he uray wordo asa attiin tumay he uran dena.
Mutumin da ya ce, “Na san shi,” amma ba ya yin abin da ya umarta, maƙaryaci ne, gaskiya kuwa ba ta cikinsa.
5 Qase oonikka iza qaala nagiko tumu Xoossa siqqoy he 7uran polletides. Nuni izan dizaysa erizay hessankko.
Amma in wani ya yi biyayya da maganarsa, ƙaunar Allah ta zama cikakkiya ke nan a cikinsa. Ta haka muka san cewa muna cikinsa.
6 Ta izan days giza uray oonikka Yesuss simeretida mala simeristanas beeses.
Duk wanda ya ce yana rayuwa a cikinsa dole yă yi tafiya kamar yadda Yesu ya yi.
7 Ta siqoto! ta intes xahaaththaizaysi kasse intes dizaro intekon gam77ida azazoyo attin hara ooratha azazo gidena. Gam77ida azazoya kasse inte siyda qaalako.
Abokaina ƙaunatattu, ba sabon umarni nake rubuta muku ba, a’a, daɗaɗɗen umarnin nan ne, wanda kuke da shi tun farko. Wannan tsohon umarni shi ne saƙon da kuka riga kuka ji.
8 Hara bagara ta intes xahaaththaizay dhumay adhi bishin tumu poo7on gish iza achanka inte achan tumu gidida ooratha azazoko.
Duk da haka ina rubuta muku sabon umarni; ana ganin gaskiyar umarnin a cikinsa da kuma cikinku, gama duhu yana shuɗewa, haske na gaskiya kuwa yana haskakawa.
9 Poo7on daysi gishe ba isha ixiizadey ha7ikka dhuma gidon dees.
Duk wanda ya ce yana cikin haske yana kuma ƙin ɗan’uwansa, ashe a duhu yake har yanzu.
10 Be isha siqqizadey poo7on dees; he uras dhuphe gidiza mishi denna.
Duk wanda yake ƙaunar ɗan’uwansa, a cikin hasken yake rayuwa ke nan, kuma babu wani abin da yake cikinsa da zai sa yă yi tuntuɓe.
11 Gido attin ba isha ixxizadey gidiko dhuma gidon dees; dhuman simeretes. Dhumay iza qoqisida gish izi awa biizakkone ba bizaso erena.
Amma duk wanda yake ƙin ɗan’uwansa, cikin duhu yake, yana kuma tafiya cikin duhu ke nan; bai ma san inda za shi ba, domin duhun ya makanta shi.
12 Ta nayto inte nagaray Yesus kiristoosape denddidayssan atto geetetida gish ta intes xafays.
Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin an gafarta muku zunubanku saboda sunansa.
13 Aawato! kasse koyrope dizaysa iza inte eriza gish ta intes xafays; Natethato inte iitta uraa Xala7e xoonida gish ta intes xahaaththaays.
Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kun ci nasara a kan mugun nan.
14 Natetha nayto! inte Aawa erida gish ta intes xafays. Aawato! koyrope dizaysa iza inte erida gish ta intes xafays. Natethato! inte miinota gidida gishinne Xoossa qaalay intenan diza gish inte iitta ura Xala7e xoonida gish ta intes xafays.
Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin kun san Uba. Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kuna da ƙarfi, maganar Allah kuwa tana zaune a cikinku, kun kuma ci nasara a kan mugun nan.
15 Haysa alameza woykko ha alamezan diza ay mishekka dosopite; Oonika ha alameza dosiiko Aawa siqoy izade achchan deena.
Kada ku ƙaunaci duniya, ko wani abin da yake cikinta. In wani yana ƙaunar duniya, ƙaunar Uba ba ta cikinsa.
16 Gasoykka ha alamezan dizay wuri asho amoteth ayfes loo7one dusan ceqeteth hayti alamepe attin Xoossa Aawape yizayta gidetenna.
Gama duk abin da yake na duniya, kamar sha’awace-sha’awacen mutuntaka, sha’awar idanunsa, da kuma taƙama da abin da yake da shi, yake kuma yi, ba daga wurin Uba suke fitowa ba sai dai daga duniya.
17 Alameynne alamen diza amotethi adhana shin Xoossa shene pollizayti gidikko medhinaas daana. (aiōn )
Duniya da sha’awace-sha’awacenta suna shuɗewa, amma mutumin da yake aikata nufin Allah, zai rayu har abada. (aiōn )
18 Nayto haysi wurisetha sate. Inte siyda mala Kirstosa eqetizadey yaana. Ha7ikka Kirstosara eqetiza daroti yida. Haysi wurisetha sate gididaysa nu hayssan eros.
’Ya’yana ƙaunatattu, waɗannan su ne kwanakin ƙarshe; kuma kamar yadda kuka ji cewa magabcin Kiristi yana zuwa, ko yanzu ma abokan gāban Kiristi da yawa sun zo. Ta haka muka san cewa kwanakin ƙarshe sun iso.
19 Isti nu gidofe kezida. Gido attin isti kasseka bagga gidettena. Istti nu bagga gididakko nunara miinni eqqanakoshin; Gido attin istti wuri nu bagga gidontaysi eretana mala nuupe shaaketida
Waɗannan masu gāba da Kiristi suna cikinmu a dā, amma sun bar mu, don tun dā ma su ba namu ba ne. Ai, da su namu ne, da har yanzu suna tare da mu. Amma sun bar mu, wannan ya nuna a fili cewa su ba namu ba ne.
20 Intena qasse Kirstossay xiillo ayanan tiyides; Hessa gish inte wurikka tuma ereista.
Amma ku kam, kuna da shafewa daga wurin Mai Tsarkin nan, kuma dukanku kun san gaskiya.
21 Ta intes xafizay inte tuma eronta gish gidena. Gido attin inte tuma eriza gishinne tuma garisafe ayko wordoyka betonttaysa inte eriza gishasa.
Ina rubuta muku ba domin ba ku san gaskiya ba ne, a’a, sai dai domin kun santa, kun kuma san cewa babu yadda ƙarya za tă fito daga gaskiya.
22 Yesussa izi Kirstossa gidena gi kadizadefe hara wordanchay oone? He uray Aawanne naaza kadiiza Kirstossara eqetizadeko.
Wane ne maƙaryaci? Ai, shi ne mutumin da yake mūsun cewa Yesu shi ne Kiristi. Irin wannan mutum shi ne magabcin Kiristi, ya yi mūsun Uban da kuma Ɗan.
23 Naaza kadizades oonasika Aaway deena; Naaza ekizades wurisos izas Aawayka dees.
Ba wanda yake mūsun Ɗan, sa’an nan yă ce yana da Uban; duk wanda ya yarda da Ɗan, yana da Uban a cikinsa ke nan.
24 Inte koyro siyda qalaya intenan du; inte koyro siydara intenan diko intekka nazanne aawan daana.
Ku lura fa cewa abin da kuka ji daga farko, bari yă ci gaba da kasance a cikinku. In kuwa ya ci gaba da zama a cikinku, za ku kasance a cikin Ɗan, da kuma a cikin Uban.
25 Medhina deyoyi izi nuus immana gida ufaysa qaalako. (aiōnios )
Wannan shi ne abin da ya yi mana alkawari, wato, rai madawwami. (aiōnios )
26 Intena balethiza asata gish hayssa intes xafadis.
Ina rubuta muku waɗannan abubuwa ne game da waɗanda suke ƙoƙari su sa ku kauce.
27 Inte qase izape ekida xiillo ayanay intenan diza gish haray oonikka intena tamarisanas bessena. Izi intena tamarisanays tumu attin worido gidena; Hessa gish xiillo ayanay intena tamarisida mala kirstoosana deyite.
Game da ku kuwa, shafan nan da kuka karɓa daga gare shi tana nan a cikinku, ba kwa kuma bukata wani yă koyar da ku. Amma kamar yadda shafan nan tasa tana koya muku kome, ita kuwa gaskiya ce ba ƙarya ba, yadda dai ta koya muku, to, sai ku zauna a cikinsa.
28 Hesa gish nayto izi qonciza wode nusu xalatethi danamala izi yiza wodeka nu iza sinthan yeletonta mala inte izan deyte.
Yanzu fa, ya ku’ya’yana ƙaunatattu, sai ku ci gaba a cikinsa, domin sa’ad da ya bayyana, mu iya tsaya gabagadi babu kunya a dawowarsa.
29 Izi xiillo gididaysa inte eriza gidiko xiillo oothizay wuri izape yelletidaysa inte ereta.
In kun san cewa shi mai adalci ne, to, kun dai san cewa duk mai aikata abin da yake daidai haifaffensa ne.