< Zacharie 2 >
1 Et je levai les yeux, et je vis; et voilà un homme, et dans sa main un cordeau d’arpenteur.
Sa’an nan na ɗaga kai sai na ga mutum a tsaye riƙe da ma’auni a hannunsa!
2 Et je dis: Où vas-tu? Et il me répondit: Mesurer Jérusalem, et voir quelle est sa largeur et quelle est sa longueur.
Sai na yi tambaya, na ce, “Ina za ka?” Ya amsa mini ya ce, “Zan je in auna Urushalima, in ga yadda fāɗinta da tsawonta suke.”
3 Et voilà que l’ange qui parlait en moi sortit, et un autre ange sortait à sa rencontre.
Sai mala’ikan da yake yi mini magana ya tafi, sai wani mala’ika ya zo ya same shi
4 Et il lui dit: Cours, parle à ce jeune homme, en disant: Jérusalem sera habitée sans mur, à cause de la multitude des hommes et des troupeaux qui seront au milieu d’elle.
ya ce masa, “Yi gudu, gaya wa saurayin can cewa, ‘Urushalima za tă zama birni marar katanga domin mutane da dabbobi masu yawa ƙwarai za su kasance a cikinta.
5 Et moi je lui serai, dit le Seigneur, un mur de feu tout autour, et je serai dans la gloire au milieu d’elle.
Ni da kaina ne zan zama katangar wuta kewaye da birnin, in kuma zama darajarta,’ in ji Ubangiji.
6 Ah! ah! fuyez de la terre de l’aquilon, dit le Seigneur; parce que vers les quatre vents du ciel, je vous ai dispersés, dit le Seigneur.
“Zo! Zo! Ku gudu daga ƙasar arewa,” in ji Ubangiji, “gama na warwatsa ku a kusurwoyi huɗu na sama,” in ji Ubangiji.
7 Fuis, ô Sion, qui habites chez la fille de Babylone.
“Zo, ya ke Sihiyona! Ku tsere, ku masu zama a cikin Diyar Babilon!”
8 Parce que voici ce que dit le Seigneur des armées: Après la gloire établie au milieu de vous, il m’a envoyé vers les nations qui vous ont dépouillés; car celui qui vous touche, touche la prunelle de mon œil.
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Bayan ya ɗaukaka ni, ya kuma aiko ni ga ƙasashen da suka washe ku gama duk wanda ya taɓa ku ya taɓa ƙwayar idonsa ne.
9 Parce que voici que je lève ma main sur eux, et ils seront la proie de ceux qui étaient leurs esclaves; et vous reconnaîtrez que c’est le Seigneur des armées qui m’a envoyé.
Ba shakka zan tā da hannuna a kansu domin bayinsu su washe su. Sa’an nan za ku san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni.
10 Loue le Seigneur, et réjouis-toi, fille de Sion; car voici que je viens moi-même, et que j’habiterai au milieu de toi, dit le Seigneur.
“Ki yi sowa ki yi murna, ya ke Diyar Sihiyona. Gama ina zuwa, zan zauna a cikinki,” in ji Ubangiji.
11 Et beaucoup de nations s’attacheront au Seigneur en ce jour; et elles seront mon peuple, et j’habiterai au milieu de toi; et tu sauras que le Seigneur des armées m’a envoyé vers toi.
“Ƙasashe da yawa za su haɗa kai da Ubangiji a ranan nan, za su kuma zama mutanena. Zan zauna a cikinku, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku.
12 Et le Seigneur possédera Juda comme son partage dans la terre sainte, et il choisira encore Jérusalem.
Ubangiji zai gāji Yahuda a matsayin rabonsa a cikin ƙasa mai tsarki zai kuma sāke zaɓi Urushalima.
13 Que toute chair soit en silence devant la face du Seigneur; parce qu’il s’est réveillé du milieu de son habitacle saint
Ku yi tsit a gaban Ubangiji, dukanku’yan adam, gama ya taso daga wurin zamansa mai tsarki.”