< Apocalypse 3 >
1 Et à l’ange de l’église de Sardes, écris: Voici ce que dit celui qui aies sept Esprits de Dieu et les sept étoiles: Je sais tes œuvres; tu as la réputation d’être vivant, mais tu es mort.
“Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar Sardisu rubuta: ' Wadannan ne kalmomin wanda yake rike da ruhohi bakwai na Allah da taurari bakwai. “Na san abin da ka aikata. Ka yi suna cewa kana raye amma kai mattacce ne.
2 Sois vigilant, et confirme tous les restes qui étaient près de mourir; car je ne trouve pas tes œuvres pleines devant mon Dieu.
Ka farka ka karfafa abin da ya rage amma ya kusan mutuwa, domin ban sami ayyukanka cikakku a gaban Allahna ba.
3 Souviens-toi donc de ce que tu as reçu et de ce que tu as entendu, et garde-le, et fais pénitence; car si tu ne veilles, je viendrai à toi comme un voleur, et tu ne sauras à quelle heure je viendrai.
Domin haka sai ka tuna, da abubuwan da ka karba kuma kaji. Ka yi biyayya da su, ka kuma tuba. Amma idan baka farka ba, zan zo maka kamar barawo, kuma ba zaka farga da sa'ar da zan zo gaba da kai ba.
4 Tu as toutefois un petit nombre de noms à Sardes qui n’ont point souillé leurs vêtements; or ils marcheront avec moi revêtus de blanc, parce qu’ils en sont dignes.
Amma akwai sunayen mutane kadan a Sardisu wadanda basu kazantar da tufafinsu ba. Za su yi tafiya tare da ni sanye da fararen tufafi domin sun cancanta.
5 Celui qui aura vaincu sera ainsi vêtu de blanc, et je n’effacerai point son nom du livre de vie; et je confesserai son nom devant mon Père et devant ses anges.
Wanda ya yi nasara za a sanya mashi fararen tufafi, kuma ba zan taba share sunansa ba daga Littafin Rai, kuma zan fadi sunansa a gaban Ubana, da kuma gaban mala'ikunsa.
6 Que celui qui a des oreilles entende ce que l’Esprit dit aux Églises.
Bari wanda yake da kunne ya saurari abin da Ruhu ke fadawa ikilisiyoyi.”'”
7 Et à l’ange de l’église de Philadelphie, écris: Voici ce que dit le Saint et le Véritable, qui a la clef de David, qui ouvre et personne ne ferme; qui ferme et personne n’ouvre.
Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar cikin Filadelfiya rubuta: kalmomin wanda yake maitsarki ne kuma mai gaskiya - yana rike da mabudin Dauda, yana budewa babu mai rufewa, kuma inda ya rufe ba mai budewa.
8 Je sais tes œuvres. J’ai posé devant toi une porte ouverte, que personne ne peut fermer, parce que tu as peu de force, et que cependant tu as garde ma parole, et tu n’as pas renoncé mon nom.
Na san abin da ka aikata. Duba, na sa budaddiyar kofa a gabanka wanda ba mai iya rufewa. Na san kana da karamin karfi, duk da haka ka yi biyayya da maganata kuma baka yi musun sunana ba.
9 Voici que je produirai quelques-uns de la synagogue de Satan, qui se disent Juifs, et ne le sont pas, mais qui mentent. Je ferai qu’ils viennent, qu’ils adorent à tes pieds, et qu’ils sachent que je t’aime.
Duba! Wadanda ke na majami'ar Shaidan, wadanda suke cewa su Yahudawa ne; amma maimakon haka karya suke yi. Zan sa su zo su rusuna a kafafunka, kuma za su san cewa ina kaunarka.
10 Parce que tu as gardé la parole de ma patience, moi aussi je te garderai de l’heure de la tentation, qui doit venir dans tout l’univers éprouver ceux qui habitent sur la terre.
Tun da ka jure cikin hakuri ka kiyaye dokoki na, ni ma zan kiyaye ka daga sa'a ta gwaji da zata sauko kan dukan duniya, domin a gwada mazauna duniya.
11 Voici que je viens bientôt: Garde ce que tu as, de peur que quelque autre ne reçoive ta couronne.
Ina zuwa da sauri. Ka rike abin da kake da shi kamkam domin kada wani ya dauke maka rawani.
12 Celui qui aura vaincu, j’en ferai une colonne dans le temple de mon Dieu, et il n’en sortira plus; et j’écrirai sur lui le nom de mon Dieu et le nom de la cité de mon Dieu, de la nouvelle Jérusalem, qui descend du ciel d’auprès de mon Dieu, et mon nouveau nom.
Zan sa wanda ya yi nasara ya zama ginshiki a haikalin Allahna, kuma ba zai taba fita daga cikin sa ba. Zan rubuta sunan Allahna a kansa, sunan birnin Allahna (sabuwar Urushalima, mai saukowa daga sama daga wurin Allahna), da kuma sabon sunana.
13 Que celui qui a des oreilles entende ce que l’Esprit dit aux Églises.
Bari wanda yake da kunne ya ji abin da Ruhu ke gayawa ikilisiyoyi.”
14 Et à l’ange de l’église de Laodicée, écris: Voici ce que dit Amen, le témoin fidèle et véritable, qui est le principe des créatures de Dieu.
“Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar da ke Lawudikiya rubuta: 'Wadannan sune kalmomin Amin, madogara da mai shaidar gaskiya, mai mulki bisa hallittar Allah.
15 Je sais tes œuvres; tu n’es ni froid ni chaud: plût à Dieu que tu fusses froid ou chaud!
Na san abin da ka aikata, ba ka sanyi ko zafi. Naso ko da kana sanyi ko zafi!
16 Mais parce que tu es tiède, et que tu n’es ni froid ni chaud, je suis près de te vomir de ma bouche.
Amma saboda kai tsaka-tsaka ne - ba zafi ba sanyi - na kusa tofar da kai daga bakina.
17 Car tu dis: Je suis riche et opulent, et je n’ai besoin de rien; et tu ne sais pas que tu es malheureux, misérable, pauvre, aveugle et nu.
Domin ka ce, “Ni mai arziki ne, na mallaki kadarori da yawa, ba na bukatar komai.” Amma ba ka sani ba kana cike da takaici ne, abin tausayi, matalauci, makaho kuma tsirara kake.
18 Je te conseille d’acheter de moi de l’or éprouvé au feu, afin de t’enrichir, et de te vêtir d’habits blancs, de peur que la honte de ta nudité ne paraisse; applique aussi un collyre sur tes yeux, afin que tu voies.
Saurari shawara ta: Ka sayi zinariya a wuri na wadda aka goge da wuta domin ka zama mai arziki, domin ka suturta kanka da fararen tufafi masu kyalli domin kada ka nuna kunyar tsiraicin ka, da mai domin ka shafa wa idanunka ka sami gani.
19 Pour moi, je reprends et je châtie ceux que j’aime. Rallume donc ton zèle, et fais pénitence.
Ina horar da duk wanda nake kauna, ina kuma koya masu yadda za su yi rayuwa. Saboda haka, ka himmatu ka tuba.
20 Me voici à la porte et je frappe; si quelqu’un entend ma voix et m’ouvre la porte, j’entrerai chez lui, et je souperai avec lui, et lui avec moi.
Duba, ina tsaye a bakin kofa ina kwankwasawa. Idan wani ya ji muryata ya bude kofar, zan shigo cikin gidansa, in ci tare da shi, shi kuma tare da ni.
21 Celui qui aura vaincu, je le ferai asseoir avec moi sur mon trône; comme moi j’ai vaincu aussi, et me suis assis avec mon Père sur son trône.
Wanda ya ci nasara, zan bashi dama ya zauna tare da ni bisa kursiyina, kamar yadda nima na ci nasara kuma na zauna da Ubana a kan kursiyinsa.
22 Que celui qui a des oreilles entende ce que l’Esprit dit aux Églises.
Bari wanda yake da kunne ya saurari abin da Ruhu yake fadawa wa ikilisiyoyi.”