< Apocalypse 17 >

1 Alors vint un des sept anges qui avaient les sept coupes, et il me parla, disant: Viens, je te montrerai la condamnation de la grande prostituée, qui est assise sur les grandes eaux,
Daya daga cikin mala'ikun nan bakwai wanda ke rike da tasoshi bakwai ya zo ya ce mani, “Zo, zan nuna maka hukuncin babbar karuwarnan da ke zaune a kan ruwaye masu yawa.
2 Avec laquelle les rois de la terre se sont corrompus, et les habitants de la terre se sont enivrés du vin de sa prostitution.
Da ita ce sarakunan duniya suka yi fasikanci. Da ruwan inabinta na fasikanci marar dacewa ta sa mazaunan duniya suka bugu.”
3 Il me transporta en esprit dans un désert, et je vis une femme assise sur une bête de couleur d’écarlate, pleine de noms de blasphème, ayant sept têtes et dix cornes.
Sai mala'ikan ya dauke ni cikin Ruhu ya tafi da ni jeji, sai na ga mace zaune bisa jan dabba cike da sunayen sabo. Dabbar tana da kawuna bakwai da kahonni goma.
4 La femme était vêtue de pourpre et d’écarlate, parée d’or, de pierres précieuses et de perles, ayant en sa main une coupe d’or pleine de l’abomination et de l’impureté de sa fornication,
Matar kuwa tana sanye da tufafi na shunayya da kuma jar garura, ta kuma ci ado da kayan zinariya da duwatsu masu tamani da lu'u-lu'ai. Tana rike da kokon zinariya a hannunta cike da abubuwan kyama da na kazantar fasikancinta marar dacewa.
5 Et sur son front un nom écrit: Mystère; la grande Babylone, la mère des fornications et des abominations de la terre.
Bisa goshinta an rubuta wani suna mai boyayyar ma'ana: “Babila mai girma, uwar karuwai da na kazamtattun abubuwan duniya.”
6 Et je vis cette femme enivrée du sang des saints et du sang des martyrs de Jésus. Or je fus surpris, quand je l’eus vue, d’un grand étonnement.
Sai na ga matar a buge da jinin masu ba da gaskiya da kuma jinin wadanda aka kashe su domin Yesu. Da na gan ta, na yi mamaki kwarai da gaske.
7 Alors l’ange me dit: Pourquoi t’étonnes-tu? C’est moi qui te dirai le mystère de la femme et de la bête qui la porte, et qui a sept têtes et dix cornes.
Amma mala'ikan ya ce mani, “Don me kake mamaki? Zan bayyana maka ma'anar matar da kuma na dabbar da ke dauke da ita, dabban nan da ke da kawuna bakwai da kahonni goma.
8 La bête que tu as vue, a été et elle n’est plus; elle doit monter de l’abîme, et elle ira à la perdition, et les habitants de la terre (dont les noms ne sont pas écrits dans le livre de vie dès la fondation du monde) seront dans l’étonnement, en voyant la bête qui était et qui n’est plus. (Abyssos g12)
Dabban da ka gani da, yanzu ba ta, amma ta na kusan hawowa daga rami marar iyaka. Sa'annan za ta je hallaka. Wadanda ke zaune a duniya, wadanda ba a rubuta sunayensu cikin littafin rai ba tun kafuwar duniya - za su yi mamaki idan suka ga dabbar da da ta kasance, ba ta nan yanzu, amma ta kusa zuwa. (Abyssos g12)
9 Or en voici le sens, lequel renferme de la sagesse: Les sept têtes sont sept montagnes, sur lesquelles la femme est assise; ce sont aussi sept rois.
Wannan al'amari na bukatar hikima. Kawunnan bakwai, tuddai ne bakwai da macen ke zaune a kai.
10 Cinq sont tombés; un existe, et l’autre n’est pas encore venu; et quand il sera venu, il faut qu’il demeure peu de temps.
Su kuma sarakuna ne bakwai. Sarakuna biyar sun fadi, daya na nan, amma dayan bai zo ba tukuna; sa'anda ya zo zai kasance na dan lokaci kadan.
11 Et la bête qui était et qui n’est plus est la huitième; elle est des sept, et elle va à la perdition.
Dabban da ya kasance a da, amma yanzu ba shi, shi ma sarki ne na takwas; amma shi daya ne cikin sarakunan nan bakwai, kuma zai tafi hallaka.
12 Les dix cornes que tu as vues sont dix rois qui n’ont pas encore reçu leur royaume; mais ils recevront la puissance comme rois pour une heure après la bête.
Kahonnin nan goma da ka gani sarakuna goma ne wadanda ba a nada su ba tukuna, amma za su karbi iko kamar na sarakai na sa'a daya tare da dabban.
13 Ceux-ci ont un même dessein, et ils donneront leur force et leur puissance à la bête.
Ra'ayinsu daya ne, za su ba da sarautarsu da ikon su ga dabban.
14 Ceux-ci combattront contre l’Agneau, mais l’Agneau les vaincra, parce qu’il est Seigneur des Seigneurs et Roi des rois; et ceux qui sont avec lui sont appelés élus et fidèles.
Za su yi yaki da Dan Rago. Dan Ragon zai ci nasara a kansu domin shi Ubangijin iyayengiji ne da Sarkin sarakuna - kuma tare da shi sune kirayayyun, zababbun, amintattun.”
15 Il me dit encore: Les eaux que tu as vues, et où la prostituée est assise, sont des peuples, des nations et des langues.
Mala'ikan ya ce mani, “Ruwayen da ka gani, inda karuwar ke zaune, jama'a ce, da taro masu dumbin yawa, da al'ummai da harsuna.
16 Les dix cornes que tu as vues dans la bête, ce sont ceux qui haïront la prostituée; ils la réduiront à la désolation et à la nudité; ils la mettront à nu, ils dévoreront ses chairs, et ils les brûleront dans le feu.
Kahonnin nan goma da ka gani - su da dabban za su ki karuwar. Za su washe ta su tsiranceta, za su lankwame namanta, za su kone ta gaba daya da wuta.
17 Car Dieu leur a mis dans le cœur de faire ce qui lui plaît; de donner leur royaume à la bête, jusqu’à ce que soient accomplies les paroles de Dieu.
Gama Allah ya sa a zukantansu su yi nufinsa ta wurin amincewarsa, su sadaukar da ikonsu na yin mulki ga dabban har sai maganar Allah ta cika.
18 Et la femme que tu as vue est la grande ville qui règne sur les rois de la terre.
Matar da ka gani ita ce babban birnin nan da ke mulki bisa sarakunan duniya.”

< Apocalypse 17 >