< Psaumes 1 >

1 Heureux l’homme qui n’est pas allé au conseil des impies, qui ne s’est pas arrêté dans la voie des pécheurs, qui ne s’est pas assis dans la chaire de pestilence;
Mai farin ciki ne mutumin da ba ya aiki da shawarar mugaye ko yă yi abin da masu zunubi suke yi ko yă zauna tare da masu yin ba’a.
2 Mais dont la volonté est dans la loi du Seigneur, et qui médite cette loi le jour et la nuit.
Amma yana jin daɗin bin dokar Ubangiji, kuma yana ta nazarinta dare da rana.
3 Il sera comme l’arbre planté près des courants des eaux, qui donnera son fruit en son temps; Et sa feuille ne tombera point; et tout ce qu’il fera prospérera.
Yana kama da itacen da aka shuka kusa da maɓulɓulan ruwa, wanda yake ba da amfani a daidai lokaci wanda kuma ganyensa ba sa bushewa. Duk abin da yake yi, yakan yi nasara.
4 Il n’en est pas ainsi des impies; non, il n’en est pas ainsi, mais ils sont comme la poussière que le vent emporte de la face de la terre.
Ba haka yake da mugaye ba! Su kamar yayi ne da iska take kwashewa.
5 C’est pourquoi les impies ne ressusciteront pas au jugement, ni les pécheurs dans l’assemblée des justes.
Saboda haka mugaye ba za su iya tsayawa a shari’a ba, balle a sami masu zunubi a taron adalai.
6 Parce que le Seigneur connaît la voie des justes, et la voie des impies périra.
Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.

< Psaumes 1 >