< Psaumes 88 >

1 Des fils de Coré, pour la fin, pour Maheleth, pour répondre, intelligence d’Eman l’Ezrahite. Seigneur, Dieu de mon salut, j’ai crié devant vous, le jour et la nuit.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Que ma prière pénètre en votre présence; inclinez votre oreille à ma supplication;
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 Parce que mon âme est remplie de maux, et que ma vie s’est approchée de l’enfer. (Sheol h7585)
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
4 J’ai été regardé comme ceux qui descendent dans une fosse: je suis devenu comme un homme sans secours,
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 Libre entre des morts,
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Ils m’ont mis dans une fosse profonde, dans des lieux ténébreux, et dans l’ombre de la mort.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Sur moi s’est fortifiée votre fureur, et vous avez fait passer tous vos flots sur moi.
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Vous avez éloigné de moi ceux qui me sont connus; ils m’ont posé comme un objet d’abomination pour eux.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 Mes yeux ont langui à cause de ma détresse.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 Est-ce que, pour des morts, vous ferez des merveilles, ou des médecins les ressusciteront-ils, afin qu’ils vous louent?
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 Est-ce que quelqu’un racontera votre miséricorde dans un sépulcre, et votre vérité dans le lieu de la destruction?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 Est-ce que vos merveilles seront connues dans les ténèbres, et votre justice dans la terre de l’oubli?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 Et moi, vers vous. Seigneur, j’ai crié, et, dès le matin, ma prière vous préviendra.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Pourquoi, Seigneur, repoussez-vous ma prière, détournez-vous votre face de moi?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 Je suis un pauvre, moi, et dans les travaux depuis ma jeunesse; et après avoir été exalté, j’ai été humilié et troublé.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Sur moi ont passé les flots de votre colère, et vos terreurs m’ont troublé.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 Elles m’ont environné, comme une eau, tout le jour, elles m’ont environné toutes ensemble.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Vous avez éloigné de moi un ami et un proche, et ceux qui m’étaient connus, à cause de ma misère.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.

< Psaumes 88 >