< Psaumes 86 >
1 Inclinez, Seigneur, votre oreille, et exaucez-moi, parce que je suis sans ressource et pauvre.
Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
2 Gardez mon âme, parce que je suis saint: sauvez, mon Dieu, votre serviteur qui espère en vous.
Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
3 Ayez pitié de moi, Seigneur, parce que vers vous j’ai crié tout le jour.
Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
4 Réjouissez l’âme de votre serviteur, parce que vers vous, Seigneur, j’ai élevé mon âme.
Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
5 Parce que vous, Seigneur, vous êtes bienveillant et doux, et d’une grande miséricorde pour tous ceux qui vous invoquent.
Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
6 Prêtez l’oreille Seigneur, à ma prière, et soyez attentif à la voix de ma supplication.
Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
7 Au jour de ma tribulation, j’ai crié vers vous, parce que vous m’avez exaucé.
A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
8 Il n’est point de semblable à vous parmi les dieux, Seigneur; et il n’est rien de comparable à vos œuvres.
A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
9 Toutes les nations que vous avez faites viendront, et adoreront devant vous, Seigneur, et glorifieront votre nom.
Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
10 Parce que vous êtes grand, vous, et que vous faites des merveilles, et que vous êtes seul Dieu.
Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
11 Conduisez-moi, Seigneur, dans votre voie, et que je marche dans votre vérité: que mon cœur se réjouisse, afin qu’il craigne votre nom.
Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
12 Je vous louerai, Seigneur mon Dieu, en tout mon cœur, et je glorifierai votre nom éternellement;
Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
13 Parce que votre miséricorde est grande envers moi, et que vous avez arraché mon âme de l’enfer le plus profond. (Sheol )
Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol )
14 Ô Dieu, des hommes iniques se sont insurgés contre moi, et une assemblée de puissants a cherché mon âme; et ils ne vous ont pas eu présent devant leurs yeux.
Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
15 Et vous, Seigneur, vous le Dieu compatissant et miséricordieux, patient, d’une grande miséricorde, et véridique,
Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
16 Jetez les yeux sur moi, et ayez pitié de moi; donnez votre puissance à votre serviteur, et sauvez le fils de votre servante.
Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
17 Faites pour moi un signe favorable, afin qu’ils le voient, ceux qui me haïssent, et qu’ils soient confondus, parce que c’est vous, Seigneur, qui m’avez aidé et consolé.
Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.