< Psaumes 84 >
1 Pour les pressoirs, aux fils de Coré, psaume. Qu’ils sont aimables, vos tabernacles, Seigneur des armées!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Na’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ina misalin kyan wurin zamanka, Ya Ubangiji Maɗaukaki!
2 Mon âme désire avec ardeur, et languit après les parvis du Seigneur. Mon cœur et ma chair ont exulté pour le Dieu vivant.
Raina yana marmari, har yana suma, don filayen gidan Ubangiji; zuciyata da namana na tā da murya domin Allah mai rai.
3 Car un passereau trouve pour lui une maison; une tourterelle, un nid où elle dépose ses petits.
Har tsada ma ta sami gida, tsatsewa kuma ta yi wa kanta sheƙa, inda za tă ƙyanƙyashe’ya’yanta, wuri kusa da bagadenka, Ya Ubangiji Maɗaukaki, Sarkina da kuma Allahna.
4 Bienheureux ceux qui habitent dans votre maison. Seigneur; dans les siècles des siècles ils vous loueront.
Masu albarka ne waɗanda suke zama a gidanka; kullum suna ta yabonka. (Sela)
5 Bienheureux l’homme dont le secours vient de vous; il a disposé dans son cœur des degrés pour s’élever,
Masu albarka ne waɗanda ƙarfinsu yana daga gare ka, waɗanda suka kafa zukatansu a yin tafiya zuwa wuri mai tsarki ne.
6 Dans la vallée de larmes, dans le lieu qu’il a fixé.
Yayinda suke wuce ta Kwarin Baka, sukan mai da shi wurin maɓulɓulai; ruwan sama na farko kuma kan rufe shi da tafkuna.
7 Car le législateur donnera sa bénédiction; ils iront de vertu en vertu; il sera vu le Dieu des dieux dans Sion.
Suna ta ƙara ƙarfi, har sai kowanne ya bayyana a gaban Allah a Sihiyona.
8 Seigneur, Dieu des armées, exaucez ma prière, prêtez l’oreille, Dieu de Jacob.
Ka ji addu’ata, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka saurare ni, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
9 Dieu notre protecteur, regardez, jetez les yeux sur la face de votre Christ;
Ka dubi garkuwarmu, ya Allah; ka duba da alheri a kan shafaffenka.
10 Parce que mieux vaut un jour passé dans vos parvis, que des milliers dans d’autres.
Rana guda a filayen gidan sun fi dubu a wani wuri dabam; zan gwammaci in zama mai tsaron ƙofa a gidan Allahna da in zauna a tentunan mugaye.
11 Parce que Dieu aime la miséricorde et la vérité, le Seigneur donnera la grâce et la gloire.
Gama Ubangiji Allah rana ne da kuma garkuwa; Ubangiji yakan yi alheri da kuma daraja; ba ya hana kowane abu mai kyau wa waɗanda suke aikata abin da yake daidai.
12 Il ne privera pas de biens ceux qui marchent dans l’innocence. Seigneur des armées, bienheureux l’homme qui espère en vous.
Ya Ubangiji Maɗaukaki, mai albarka ne mutumin da ya dogara gare ka.