< Psaumes 78 >
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 J’ouvrirai ma bouche en paraboles: je dirai des choses cachées dès le commencement;
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 Combien de grandes choses nous avons entendu et connues, et que nos pères nous ont racontées.
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 Elles n’ont pas été cachées à leurs fils dans une autre génération. Ils ont raconté les louanges du Seigneur, ses œuvres puissantes, et ses merveilles qu’il a faites;
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Et a suscité un témoignage dans Jacob; et a établi une loi dans Israël: Combien de grandes choses il a commandé à nos pères de faire connaître à leurs fils,
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 Afin qu’une autre génération les connaisse. Les fils qui naîtront et s’élèveront après eux les raconteront à leurs fils,
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 Afin qu’ils mettent en Dieu leur espérance, qu’ils n’oublient pas ses œuvres, et qu’ils recherchent ses commandements.
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 De peur qu’ils ne deviennent comme leurs pères une génération perverse et exaspérant Dieu; Une génération qui n’a point dirigé son cœur, et dont l’esprit ne s’est point confié en Dieu.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 Les fils d’Ephraïm, habiles à tendre l’arc et à en tirer, ont tourné le dos au jour du combat.
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 Ils n’ont pas gardé l’alliance de Dieu, et ils n’ont pas voulu marcher dans sa loi.
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 Ils ont oublié ses bienfaits et les merveilles qu’il leur a montrées.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 Devant leurs pères il a fait des merveilles, dans la terre d’Égypte, dans la plaine de Tanis.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Il divisa la mer, et il les fit passer: et il fixa les eaux comme dans une outre.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 Il les conduisit, le jour, au moyen d’une nuée, et toute la nuit à la clarté d’un feu.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 Il fendit une pierre dans le désert, et les fit boire comme à un abîme abondant.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 Car il fit sortir de l’eau de la pierre, et il en fit sortir des eaux comme des fleuves.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 Mais ils péchèrent encore de nouveau contre lui, ils excitèrent à la colère le Très-Haut dans un lieu sans eau.
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 Et ils tentèrent Dieu dans leurs cœurs, au point qu’ils demandèrent une nourriture pour leurs âmes.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 Et ils parlèrent mal de Dieu, ils dirent: Est-ce que Dieu pourra préparer une table dans le désert?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Parce qu’il a frappé une pierre, et que des eaux ont coulé; et que des torrents ont débordé. Est-ce qu’il pourra aussi donner du pain et préparer une table pour son peuple?
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 C’est pour cela que le Seigneur entendit et différa; mais un feu s’alluma contre Jacob, et sa colère monta contre Israël;
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 Parce qu’ils ne crurent pas en Dieu, et qu’ils n’espérèrent pas en son salut;
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Et il commanda aux nuées d’en haut, et il ouvrit les portes du ciel.
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 Et il leur fit pleuvoir de la manne pour manger, et il leur donna du pain du ciel.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 L’homme mangea le pain des anges, Dieu leur envoya une nourriture en abondance.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Il fit disparaître du ciel le vent du midi, et il amena par sa puissance le vent d’Afrique.
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 Il fit pleuvoir sur eux des viandes comme la poussière, et des oiseaux comme le sable de la mer.
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 Et ils tombèrent au milieu de leur camp, autour de leurs tabernacles.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 Ils mangèrent et ils furent rassasiés à l’excès, et Dieu leur accorda selon leur désir;
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 Ils ne furent point frustrés dans leur désir. Leurs viandes étaient encore dans leur bouche,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 Quand la colère de Dieu tomba sur eux. Et il tua les gras d’entre eux, et rejeta l’élite d’Israël.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 Au milieu de tous ces prodiges ils péchèrent encore, et ne crurent pas à ses merveilles.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Et leurs jours se terminèrent vainement, et leurs années avec rapidité.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Lorsqu’il les tuait, ils le cherchaient, et ils revenaient, et, dès le point du jour, ils venaient à lui.
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 Et ils se souvinrent que Dieu était leur aide, et que le Dieu très haut était leur rédempteur.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Mais ils l’aimèrent de bouche seulement, et ils lui mentirent par leur langue;
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 Car leur cœur n’était pas droit avec lui, et ils ne furent pas trouvés fidèles à son alliance.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Mais lui est miséricordieux, il pardonnera leurs péchés, et ne les perdra pas entièrement. Et souvent il détourna sa colère, et il n’alluma pas toute sa colère.
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 Il se rappela qu’ils étaient chair, un souffle qui va et qui ne revient pas.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Combien de fois l’ont-ils irrité dans le désert, et l’ont-ils excité à la colère dans un lieu sans eau?
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 Et de nouveau ils tentèrent Dieu, et ils ont aigri le saint d’Israël.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 Ils ne se sont pas rappelé sa main, au jour où il les retira de la main d’un oppresseur,
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 Comment il fit en Égypte ses miracles, et ses prodiges dans la plaine de Tanis.
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 Et il changea en sang leurs fleuves et leurs pluies, pour qu’ils ne bussent point.
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 Il envoya contre eux une multitude de mouches qui les dévorèrent, et la grenouille qui les ravagea.
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 Et il donna à la rouille leurs fruits, et leurs travaux à la sauterelle.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 Et il fit périr par la grêle leurs vignes, et leurs mûriers par la gelée.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 Et il livra à la grêle leurs bêtes, et leurs possessions au feu.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 Il envoya contre eux la colère de son indignation: l’indignation, et la colère, et la tribulation envoyées par des anges mauvais.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 Il fit une voie au sentier de sa colère, et il n’épargna pas la mort à leurs âmes; et leurs bêtes, il les renferma dans la mort.
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 Et il frappa tout premier-né d’Égypte, les prémices de tout travail dans les tabernacles de Cham.
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 Et il en retira, comme des brebis, son peuple; et il les conduisit comme un troupeau dans le désert.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 Et il les fit sortir pleins d’espérance, et ils ne craignirent point; quant à leurs ennemis, la mer les couvrit.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 Et il les amena sur la montagne de sa sanctification; montagne qu’a acquise sa droite. Et il chassa de leur face des nations; et il leur divisa au sort une terre avec un cordeau de partage.
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 Et il fit habiter dans leurs tabernacles les tribus d’Israël.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Mais ils tentèrent et aigrirent le Dieu très haut; et ne gardèrent pas ses témoignages.
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 Et ils se détournèrent de lui et n’observèrent pas l’alliance; de la même manière que leurs pères, ils devinrent comme un arc qui porte à faux.
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 Ils l’ont excité à la colère sur leurs collines; et par leurs images taillées au ciseau, ils l’ont provoqué à la jalousie.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 Dieu entendit, et il méprisa, et il réduisit entièrement au néant Israël.
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 Et il repoussa le tabernacle de Silo, son tabernacle où il avait habité parmi les hommes.
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 Il livra à la captivité l’arche, leur force; et leur beauté entre les mains de l’ennemi.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 Il renferma son peuple entre les glaives; et son héritage, il le méprisa.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Un feu dévora leurs jeunes hommes; et leurs vierges ne furent pas pleurées.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 Leurs prêtres tombèrent sous le glaive, et on ne pleurait pas leurs veuves.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Mais le Seigneur se réveilla comme un homme endormi, comme un héros qui a été ivre de vin.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 Il frappa ses ennemis par derrière; il leur infligea un opprobre éternel.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Et il repoussa le tabernacle de Joseph, et ne choisit point la tribu d’Éphraïm;
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 Mais il choisit la tribu de Juda, la montagne de Sion qu’il a aimée.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 Et il bâtit comme une corne de licornes son sanctuaire, dans la terre qu’il a fondée pour les siècles.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 Il choisit David son serviteur, et il le tira du milieu des troupeaux de brebis: il le prit à la suite de celles qui étaient pleines,
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 Pour être le pasteur de Jacob son serviteur, et d’Israël son héritage.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Et David les fit paître dans l’innocence de son cœur, et avec ses mains habiles, il les conduisit.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.