< Psaumes 73 >
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 Mais mes pieds ont presque chancelé, et mes pas ont presque dévié.
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 Parce que j’ai porté envie aux hommes iniques, voyant la paix des pécheurs.
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 Parce qu’ils ne pensent pas à leur mort, et que leur plaie n’a pas de consistance.
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 Ils ne seront pas sujets à la fatigue des hommes, et avec les autres hommes ils ne seront pas frappés;
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 C’est pour cela que l’orgueil s’est emparé d’eux, qu’ils se sont couverts de leur iniquité et de leur impiété.
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 Leur iniquité est sortie comme de leur graisse; ils ont suivi le sentiment de leur cœur.
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 Ils ont pensé et ils ont parlé méchanceté; ils ont parlé hautement iniquité.
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 Ils ont posé leur bouche contre le ciel, et leur langue a passé sur la terre.
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 C’est pour cela que mon peuple en reviendra là: et les impies trouveront en eux des jours pleins.
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 Et ils ont dit: Comment Dieu le sait-il? et le Très-Haut en a-t-il connaissance?
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 Voilà que ces pécheurs eux-mêmes, vivant dans l’abondance, ont obtenu des richesses.
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 Et j’ai dit: C’est donc sans cause que j’ai purifié mon cœur, et que j’ai lavé mes mains parmi des innocents.
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 Car j’ai été affligé tout le jour, et mon châtiment a eu lieu les matins.
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 Si je disais: Je parlerai ainsi, voilà que je réprouvais la race de vos enfants.
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 Je pensais à connaître ce mystère: un pénible travail s’est trouvé devant moi.
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 Jusqu’à ce que j’entre dans le sanctuaire de Dieu, et que je comprenne leurs fins dernières.
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 Mais cependant à cause de leurs tromperies vous leur avez envoyé des maux; vous les avez renversés, tandis qu’ils s’élevaient.
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 Comment sont-ils tombés dans la désolation? Soudain ils ont défailli: ils ont péri à cause de leur iniquité.
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 Comme un songe de ceux qui s’éveillent. Seigneur, vous réduirez au néant leur image dans votre cité.
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 Parce que mon cœur a été enflammé, et que mes reins ont été bouleversés;
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 Et que moi j’ai été réduit au néant, et que je n’ai pas su pourquoi.
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 Que je suis devenu comme un animal stupide devant vous, mais que toujours j’ai été avec vous.
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 Vous avez soutenu ma main droite: selon votre volonté vous m’avez dirigé, et vous m’avez reçu avec gloire.
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 Car qu’y a-t-il pour moi dans le ciel, et hors de vous qu’ai-je voulu sur la terre?
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 Ma chair a défailli, ainsi que mon cœur; ô le Dieu de mon cœur, et le Dieu mon partage pour l’éternité!
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 Parce que voilà que ceux qui s’éloignent de vous périront: vous avez perdu tous ceux qui forniquent, en s’éloignant de vous.
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 Pour moi, mon bien est de m’attacher à Dieu, de mettre dans le Seigneur Dieu mon espérance; Afin que j’annonce toutes vos louanges aux portes de la ville de Sion.
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.