< Psaumes 7 >

1 Psaume de David qu’il chanta au Seigneur, à cause des paroles de Chus, fils de Jémini. Seigneur, mon Dieu, c’est en vous que j’ai espéré; sauvez-moi de tous ceux qui me persécutent et délivrez-moi.
Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
2 De peur qu’enfin, comme un lion, il ne ravisse mon âme, tandis qu’il n’y a personne qui me délivre et me sauve.
in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
3 Seigneur mon Dieu, si j’ai fait cela, si l’iniquité est dans mes mains;
Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
4 Si j’ai rendu le mal à ceux qui m’en avaient fait, que je tombe devant mes ennemis sans défense; je l’ai mérité.
in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
5 Que l’ennemi poursuive mon âme, qu’il la saisisse, et qu’il foule ma vie contre la terre, et qu’il ensevelisse ma gloire dans la poussière.
to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
6 Levez-vous, Seigneur, dans votre colère, et paraissez dans votre grandeur au milieu de mes ennemis. Levez-vous, Seigneur mon Dieu, selon le précepte que vous avez établi.
Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
7 Et l’assemblée des peuples vous environnera. Et à cause d’elle retournez en haut.
Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
8 Le Seigneur juge les peuples. Jugez-moi, Seigneur, selon ma justice, et selon l’innocence qui est en moi.
bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
9 La méchanceté des pécheurs sera anéantie, et vous dirigerez le juste, ô Dieu qui sondez les cœurs et les reins.
Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
10 Un juste secours me viendra du Seigneur, qui sauve les hommes droits de cœur.
Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
11 Dieu est un juge équitable, fort et patient; est-ce qu’il s’irrite tous les jours?
Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
12 Si vous ne vous convertissez, il fera vibrer son glaive; il a tendu son arc, et il l’a préparé.
In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
13 Il y a adapté des instruments de mort, il a préparé ses flèches contre les ardents persécuteurs.
Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
14 Voilà qu’il a enfanté l’injustice: il a conçu la douleur et a mis au monde l’iniquité.
Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
15 Il a ouvert un abîme, et il l’a creusé; et il est tombé dans la fosse qu’il avait faite.
Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
16 La douleur qu’il voulait me causer retournera sur sa tête; et son iniquité descendra sur lui.
Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
17 Je louerai le Seigneur selon sa justice; je chanterai le nom du Dieu très-haut.
Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.

< Psaumes 7 >