< Psaumes 66 >

1 Cantique d’un psaume de résurrection. Poussez des cris de joie vers Dieu, ô terre tout entière;
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Dites un psaume à l’honneur de son nom: rendez gloire à sa louange.
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Dites à Dieu: Que vos œuvres sont redoutables, Seigneur! à la vue de la grandeur de votre puissance, vos ennemis vous mentiront.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 Que toute la terre vous adore et vous chante; qu’elle dise un psaume à la gloire de votre nom.
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Venez et voyez les œuvres de Dieu: il est terrible dans ses desseins sur les fils des hommes.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 C’est lui qui a changé la mer en une terre aride: ils passeront dans un fleuve à pied sec, là nous nous réjouirons.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 C’est lui qui domine éternellement par sa puissance: ses yeux regardent les nations: que ceux qui l’irritent ne s’élèvent pas en eux-mêmes.
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Bénissez, ô nations, notre Dieu, faites entendre la voix de sa louange.
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 C’est lui qui a rendu mon âme à la vie, et qui n’a pas permis que mes pieds aient chancelé.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 Parce que vous nous avez éprouvés, ô Dieu, vous nous avez épurés par le feu, comme l’argent est épuré.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 Vous nous avez conduits dans le lacs, vous avez mis des tribulations sur nos épaules:
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 Vous avez imposé des hommes sur nos têtes.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 J’entrerai dans votre maison avec des holocaustes; je vous rendrai mes vœux,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 Qu’ont proférés mes lèvres, Et qu’a exprimés ma bouche dans ma tribulation.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 Je vous offrirai des holocaustes gras, avec la fumée des béliers: je vous offrirai des bœufs avec des boucs.
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Venez et écoutez, vous tous qui craignez le Dieu Seigneur, et je raconterai quelles grandes choses il a faites pour mon âme.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 C’est vers lui que j’ai crié de ma bouche, et c’est lui que j’ai exalté par ma langue.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 Si j’ai regardé l’iniquité dans mon cœur, le Seigneur ne m’exaucera pas.
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 C’est pour cela que le Seigneur m’a exaucé, et qu’il a été attentif à la voix de ma supplication.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Béni le Dieu qui n’a pas écarté ma prière, ni sa miséricorde de moi!
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< Psaumes 66 >