< Psaumes 62 >
1 Pour Idithun, psaume de David. Est-ce que mon âme ne sera pas soumise à Dieu? car c’est de lui-même que vient mon salut.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
2 Car lui-même est mon Dieu et mon sauveur, mon soutien, je ne serai plus ébranlé.
Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
3 Jusques à quand fondrez-vous sur un homme? chercherez- vous tous ensemble a le détruire, comme vous feriez à une muraille qui penche, et à un mur sec qui s’écroule?
Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
4 Car ils ont songé à me dépouiller de ma dignité: j’ai couru dans ma soif. De leur bouche ils me bénissaient, et de leur cœur ils me maudissaient.
Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
5 Cependant, sois soumise à Dieu, ô mon âme, puisque de lui vient ma patience.
Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
6 Parce que lui-même est mon Dieu et mon sauveur: mon aide, je n’émigrerai pas.
Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
7 En Dieu est mon salut et ma gloire: il est le Dieu de mon secours, et mon espérance est en Dieu.
Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
8 Espérez en lui, vous tous qui composez l’assemblée de son peuple; répandez devant lui vos cœurs: Dieu est notre aide pour l’éternité.
Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
9 Mais les fils des hommes sont vains; les fils des hommes sont faux dans leurs balances; afin de tromper ensemble par vanité.
Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
10 Gardez-vous bien d’espérer dans l’iniquité, et gardez-vous bien de désirer des rapines: si les richesses vous affluent, gardez-vous bien d’y attacher votre cœur.
Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
11 Dieu a parlé une fois, j’ai entendu ces deux choses: que la puissance est à Dieu,
Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
12 Et à vous, Seigneur, la miséricorde: que vous rendrez à chacun selon ses œuvres.
kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”