< Psaumes 57 >
1 Ne perdez pas entièrement; par David, pour une inscription de titre, lorsqu’il s’enfuit de devant la face de Saül dans la caverne. Ayez pitié de moi, ô Dieu, ayez pitié de moi, parce que mon âme s’est confiée en vous. Et à l’ombre de vos ailes, j’espérerai jusqu’à ce que l’iniquité soit passée.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da ya gudu daga Shawulu zuwa cikin kogo. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi mini jinƙai, gama a gare ka raina yake samun mafaka. Zan sami mafaka a inuwar fikafikanka sai masifar ta wuce.
2 Je crierai au Dieu très haut, au Dieu qui m’a fait du bien.
Na yi kuka ga Allah Mafi Ɗaukaka, ga Allah, wanda yake cika manufarsa gare ni.
3 Il a envoyé du ciel, et il m’a délivré: il a donné en opprobre ceux qui me foulaient aux pieds. Dieu a envoyé sa miséricorde et sa vérité,
Ya aika daga sama ya kuwa cece ni, yana tsawata wa waɗanda suke fafarata da zafi; (Sela) Allah yakan aika da ƙaunarsa da amincinsa.
4 Et il a arraché mon âme du milieu des petits des lions: j’ai dormi tout troublé. Les fils des hommes, leurs dents sont des armes et des flèches, et leur langue un glaive acéré.
Ina tsakiyar zakoki; ina kwance a cikin namun jeji masu cin mutane, mutanen da haƙoransu masu ne da kuma kibiyoyi, waɗanda harshensu suna da kaifi kamar takobi.
5 Élevez-vous au-dessus des cieux, ô Dieu, et que sur toute la terre éclate votre gloire.
Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
6 Ils ont préparé un lacs pour mes pieds, et ils ont courbé mon âme. Ils ont creusé devant ma face une fosse, et ils y sont tombés.
Sun shimfiɗa raga don su kama ƙafafuna, damuwa ta sha ƙarfina. Sun haƙa rami a hanyata, amma su kansu suka fāɗa a cikinta. (Sela)
7 Mon cœur est prêt, ô Dieu, mon cœur est prêt: je chanterai et je dirai un psaume.
Zuciyata tana nan daram, ya Allah, zuciyata tana nan daram; zan rera in kuma yi kaɗe-kaɗe.
8 Lève-toi, ô ma gloire, lève-toi, psaltérion, et toi, harpe: je me lèverai au point du jour.
Ka farka, raina! Ku farka, garaya da molo! Zan sa safe yă farka.
9 Je vous louerai parmi les peuples. Seigneur, et je dirai un psaume en votre honneur parmi les nations.
Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai a cikin mutane.
10 Parce que votre miséricorde s’est élevée jusqu’aux cieux, et votre vérité jusqu’aux nues.
Gama ƙaunarka mai girma ce, tana kaiwa sammai; amincinka na kaiwa sarari.
11 Soyez exalté au-dessus des cieux, ô Dieu, et que sur toute la terre éclate votre gloire.
Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.