< Psaumes 55 >
1 Pour la fin, dans les cantiques, intelligence à David. Exaucez, ô Dieu, ma prière, et ne méprisez pas ma supplication.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
2 Portez votre attention sur moi, et exaucez-moi. J’ai été contristé dans ma méditation: et j’ai été troublé
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
3 À la voix d’un ennemi et à cause de l’oppression du pécheur. Parce qu’ils ont détourné sur moi des iniquités; et par colère ils me tourmentaient.
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
4 Mon cœur a été troublé au dedans de moi; et la frayeur de la mort est tombée sur moi.
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
5 Une crainte et un tremblement sont venus sur moi; et des ténèbres m’ont couvert.
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
6 Et j’ai dit: Qui me donnera des ailes comme les ailes d’une colombe, et je m’envolerai, et je me reposerai?
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
7 Voilà que je me suis éloigné en fuyant: et j’ai demeuré dans le désert.
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
8 J’attendais celui qui m’a sauvé d’un abattement d’esprit et d’une tempête.
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
9 Précipitez- les, Seigneur, divisez leurs langues; parce que j’ai vu l’iniquité et la discorde dans la cité.
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
10 Jour et nuit l’iniquité l’environnera sur ses murs: le travail est au milieu d’elle,
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
11 Ainsi que l’injustice. L’usure n’a pas fait défaut dans ses places publiques, ni la fraude.
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
12 Car si c’eût été mon ennemi qui m’eût maudit, je l’aurais supporté certainement. Et si celui qui me haïssait avait parlé contre moi avec hauteur, je me serais, sans doute, caché de lui.
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
13 Mais c’est toi, homme qui vivais avec moi dans un même esprit, mon guide et mon familier,
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
14 Qui partageais avec moi les doux mets de ma table; nous avons marché dans la maison du Seigneur avec un parfait accord.
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
15 Vienne la mort sur eux; et qu’ils descendent dans l’enfer tout vivants: Parce que la méchanceté est dans leurs demeures, au milieu d’eux. (Sheol )
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol )
16 Mais moi, j’ai crié vers Dieu, et le Seigneur me sauvera.
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17 Le soir, et le matin, et à midi, je raconterai et j’annoncerai ses miséricordes, et il exaucera ma voix.
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18 Il rachètera en paix mon âme de ceux qui s’approchaient de moi; car ils étaient en grand nombre avec moi.
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19 Dieu m’ exaucera, et les humiliera, lui qui est avant les siècles. Car il n’y a pas de changement en eux, et ils n’ont pas craint Dieu.
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20 Il a étendu sa main en leur rendant selon leurs mérites. Ils ont souillé son alliance,
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21 Ils ont été dissipés par la colère de son visage; et son cœur s’est approché contre eux.
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22 Déposez vos soins dans le sein du Seigneur, et lui-même vous nourrira; il ne laissera pas éternellement le juste dans l’agitation.
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
23 Mais vous, ô Dieu, vous les conduirez dans un puits de destruction. Les hommes de sang et trompeurs n’arriveront pas à la moitié de leurs jours: mais moi, j’espérerai en vous, Seigneur.
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.