< Psaumes 51 >
1 Pour la fin, psaume de David. Lorsque le prophète Nathan vint le trouver, après qu’il eut péché avec Bethsabée. Ayez pitié de moi. Seigneur, selon votre grande miséricorde; Et selon la multitude de vos bontés, effacez mon iniquité.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
2 Lavez-moi encore plus de mon iniquité, et purifiez-moi de mon péché.
Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
3 Parce que moi aussi, je connais mon iniquité, et mon péché est toujours devant moi.
Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
4 J’ai péché contre vous seul, et j’ai fait le mal devant vous: je fais cet aveu, afin que vous soyez reconnu juste dans vos paroles, et que vous soyez victorieux quand on vous juge.
Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
5 Voilà, en effet, que j’ai été conçu dans des iniquités, et que ma mère m’a conçu dans des péchés.
Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
6 Voilà, en effet, Seigneur, que vous aimez la vérité; que vous m’avez manifesté les choses obscures et cachées de votre sagesse.
Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
7 Vous m’aspergerez avec de l’hysope et je serai purifié; vous me laverez, et je deviendrai plus blanc que la neige.
Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
8 Vous me ferez entendre une parole de joie et d’ allégresse, et mes os humiliés exulteront.
Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
9 Détournez votre face de mes péchés; et effacez toutes mes iniquités.
Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
10 Créez un cœur pur en moi, ô mon Dieu! et renouvelez un esprit droit dans mes entrailles.
Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
11 Ne me rejetez pas de devant votre face, et ne me retirez pas votre esprit saint de moi.
Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
12 Rendez-moi la joie de votre salut, et par votre esprit souverain fortifiez-moi.
Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
13 J’enseignerai aux hommes iniques vos voies, et les impies se convertiront à vous.
Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
14 Délivrez-moi d’un sang versé, ô Dieu, Dieu de mon salut: et ma langue publiera avec joie votre justice.
Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
15 Seigneur, vous ouvrirez mes lèvres, et ma bouche annoncera votre louange.
Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
16 Parce que si vous aviez voulu un sacrifice, je vous l’aurais offert certainement; mais des holocaustes ne vous seront point agréables.
Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
17 Le sacrifice que Dieu désire est un esprit brisé de douleur: vous ne dédaignerez pas, ô Dieu, un cœur contrit et humilié.
Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
18 Dans votre bonne volonté, Seigneur, traitez bénignement Sion; et que les murs de Jérusalem soient bâtis.
Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
19 Alors vous agréerez un sacrifice de justice, des oblations et des holocaustes; alors on mettra sur votre autel des veaux.
Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.