< Psaumes 49 >

1 Pour la fin, aux fils de Coré, psaume. Écoutez ces choses, vous toutes, nations: prêtez l’oreille, vous qui habitez l’univers;
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
2 Vous tous, fils de la terre, et fils des hommes, ensemble et de concert, riche et pauvre.
babba da yaro mai arziki da talaka.
3 Ma bouche parlera sagesse, et la méditation de mon cœur, prudence.
Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
4 J’inclinerai mon oreille à une parabole, et je révélerai sur le psaltérion mon sujet.
Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
5 Pourquoi craindrai-je au jour mauvais? Je craindrai si l’iniquité de ma voie m’environne.
Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
6 Qu’ils craignent ceux qui se confient dans leur puissance, et se glorifient dans l’abondance de leurs richesses.
waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
7 Un frère ne rachète pas son frère: un homme étranger le rachètera-t-il? il ne donnera pas à Dieu de quoi l’apaiser pour lui-même,
Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
8 Ni le prix du rachat de son âme: et il travaillera éternellement.
kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
9 Et il vivra encore jusqu’à la fin.
da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
10 Il ne verra pas la mort, lorsqu’il aura vu les sages mourir: l’insensé et le fou périront également. Et ils laisseront à des étrangers leurs richesses.
Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
11 Et leurs sépulcres seront leurs maisons pour toujours. Et leurs tabernacles dans chaque génération; quoiqu’ils aient donné leurs noms à leurs terres.
Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
12 Et l’homme, lorsqu’il était en honneur, ne l’a pas compris: il a été comparé aux animaux sans raison, et il est devenu semblable à eux.
Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
13 Cette voie qu’ils suivent est une pierre d’achoppement pour eux-mêmes, et néanmoins dans la suite ils se complairont dans leurs discours.
Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
14 Comme des brebis, ils ont été parqués dans l’enfer: c’est la mort qui les paîtra. (Sheol h7585)
Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
15 Mais cependant Dieu rachètera mon âme de la main de l’enfer, quand il m’aura pris sous sa protection. (Sheol h7585)
Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
16 Ne craignez pas lorsqu’un homme sera devenu riche, et que la gloire de sa maison se sera accrue.
Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
17 Parce que, lorsqu’il sera mort, il n’emportera pas tous ses biens; et que sa gloire ne descendra pas avec lui.
gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
18 Car son âme, pendant sa vie, sera bénie: il vous louera, lorsque vous lui aurez fait du bien.
Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
19 Il ira rejoindre les générations de ses pères, et durant l’éternité, il ne verra pas la lumière.
zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
20 L’homme, lorsqu’il était en honneur, ne l’a pas compris: il a été comparé aux animaux sans raison, et il est devenu semblable à eux.
Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.

< Psaumes 49 >