< Psaumes 46 >

1 Pour la fin, aux fils de Coré, pour les secrets, psaume. Dieu est notre refuge et notre force, notre aide dans les tribulations qui nous ont assaillis très violemment.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Bisa ga alamot Waƙa ce. Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, kullum yana a shirye yă taimaka a lokacin wahala.
2 C’est pour cela que nous ne craindrons pas, tandis que la terre sera bouleversée, et que des montagnes seront transportées au cœur des mers,
Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, ko da ƙasa ta girgiza duwatsu kuma suka fāɗi cikin zurfin teku,
3 Leurs flots ont mugi et ont été agités: les montagnes ont été ébranlées par la puissance de Dieu.
ko da ruwansa suna ruri suna kumfa duwatsu kuma suna girgiza da tumbatsansu. (Sela)
4 Le cours d’un fleuve abondant réjouit la cité de Dieu; le Très-Haut y a sanctifié son tabernacle.
Akwai kogi mai rafuffukan da suke sa birnin Allah murna, tsattsarkan wuri inda Mafi Ɗaukaka ke zama.
5 Dieu est au milieu de cette cité, elle ne sera pas ébranlée: Dieu la protégera dès le matin, au lever de l’aurore.
Allah yana cikinta, ba za tă fāɗi ba; Allah zai taimake ta da safe.
6 Des nations ont été troublées et des royaumes ont chancelé: il a fait entendre sa voix, et la terre a été ébranlée.
Al’ummai suna hayaniya, mulkoki sun fāɗi; ya ɗaga muryarsa, duniya ta narke.
7 Le Seigneur des armées est avec nous: le Dieu de Jacob est notre soutien.
Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
8 Venez, et voyez les œuvres du Seigneur, vrais prodiges qu’il a opérés sur la terre,
Zo ku ga ayyukan Ubangiji, kangon da ya kawo a kan duniya.
9 En faisant cesser les guerres jusqu’à l’extrémité de la terre. Il brisera l’arc, mettra les armes en pièces; et les boucliers, il les brûlera dans le feu.
Ya sa yaƙoƙi suka yi tsit ko’ina a duniya. Ya kakkarya bakkuna ya kuma ragargaza māsu, ya ƙone garkuwoyi da wuta.
10 Tenez-vous en repos, et voyez que c’est moi qui suis Dieu; je serai exalté parmi les nations; et je serai exalté par toute la terre.
“Ku natsu ku kuma san cewa ni ne Allah; za a ɗaukaka ni a cikin al’ummai, za a ɗaukaka ni cikin duniya.”
11 Le Seigneur des armées est avec nous: notre soutien est le Dieu de Jacob.
Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)

< Psaumes 46 >