< Psaumes 21 >

1 Pour la fin, psaume de David. Seigneur, dans votre force le roi se réjouira, et à cause de votre salut, il tressaillira de la plus vive allégresse.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
2 Vous lui avez accordé le désir de son cœur; et vous n’avez pas trompé le vœu de ses lèvres;
Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
3 Puisque vous l’avez prévenu des bénédictions les plus douces; vous avez mis sur sa tête une couronne de pierres précieuses.
Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
4 Il vous a demandé la vie; et vous lui avez accordé une longueur de jours jusqu’à un siècle, et jusqu’à un siècle de siècles.
Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
5 Grande est sa gloire par votre salut; vous l’avez couvert de gloire et de beauté.
Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
6 Car vous en ferez un objet de bénédiction pour les siècles des siècles: vous le remplirez de joie par la vue de votre visage.
Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
7 Parce que le roi espère dans le Seigneur et dans la miséricorde du Très-Haut, il sera inébranlable.
Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
8 Que votre main se trouve sur tous vos ennemis; que votre droite trouve tous ceux qui vous haïssent.
Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
9 Vous les rendrez comme une fournaise ardente, au temps de votre visage: le Seigneur dans sa colère les jettera dans le trouble, et un feu les dévorera.
A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
10 Vous ferez disparaître son fruit de la terre, et sa semence d’entre les fils des hommes.
Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
11 Parce qu’ils ont voulu faire tomber des maux sur vous; ils ont conçu des desseins qu’ils n’ont pu exécuter.
Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
12 Parce que vous leur ferez tourner le dos: quand à ceux que vous laisserez survivre, vous disposerez leur visage à recevoir vos traits.
gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
13 Élevez-vous, Seigneur, dans votre force, nous chanterons et nous célébrerons par des hymnes les merveilles de votre puissance.
Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.

< Psaumes 21 >