< Psaumes 18 >
1 Pour la fin, par le serviteur du Seigneur, David, qui a prononce à la gloire du Seigneur les paroles de ce cantique, au jour où le Seigneur l’arracha à la main de ses ennemis, et à la main de Saül, et a dit: Je vous aimerai, Seigneur, ma force:
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
2 Le Seigneur est mon ferme appui, et mon refuge, et mon libérateur.
Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
3 En le louant, j’invoquerai le Seigneur, et je serai sauvé de mes ennemis.
Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
4 Les douleurs de la mort m’ont environné; les torrents de l’iniquité m’ont troublé.
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
5 Les douleurs de l’enfer m’ont environné; les lacs de la mort m’ont prévenu. (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
6 Dans ma tribulation j’ai invoqué le Seigneur, et j’ai crié vers mon Dieu;
Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
7 La terre s’est émue et a tremblé; les fondements des montagnes ont été bouleversés et ébranlés, parce qu’il s’est irrité contre eux.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
8 La fumée a monté dans sa colère, et un feu ardent a jailli de sa face; des charbons en ont été embrasés.
Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
9 Il a incliné les cieux, et il est descendu; et un nuage obscur est sous ses pieds.
Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
10 Et il est monté sur des chérubins et il s’est envolé; il s’est envolé sur les ailes des vents.
Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
11 Et il a fait des ténèbres son lieu de retraite; autour de lui est sa tente, une eau ténébreuse est dans les nuées de l’air.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
12 À l’éclat qui jaillit de sa présence, les nuées se sont dissipées; il en est sorti de la grêle et des charbons de feu.
daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
13 Et le Seigneur a tonné du ciel, et le Très-Haut a fait entendre sa voix; il est tombé de la grêle et des charbons de feu.
Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
14 Et il a lancé ses flèches, et il les a dissipés; il a multiplié ses éclairs, et il les a troublés.
Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
15 Alors ont paru les sources des eaux, et les fondements du globe de la terre ont été mis à nu, À votre menace. Seigneur, au souffle du vent de votre colère.
Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
16 Il a envoyé d’en haut, et il m’a pris, et il m’a retiré d’un gouffre d’eaux.
Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
17 Il m’a arraché à mes ennemis très puissants, et à ceux qui me haïssaient, parce qu’ils étaient devenus plus forts que moi.
Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
18 Ils m’ont prévenu au jour de mon affliction, et le Seigneur s’est fait mon protecteur.
Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
19 Et il m’a mis au large: il m’a sauvé, parce qu’il m’aimait.
Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
20 Et le Seigneur me rétribuera selon ma justice, et il me rétribuera selon la pureté de mes mains,
Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
21 Parce que j’ai gardé les voies du Seigneur, et que je n’ai pas agi avec impiété en m’éloignant de mon Dieu.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
22 Puisque tous ses jugements sont devant mes yeux, et que je n’ai point éloigné de moi ses justices.
Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
23 Et je serai sans tache avec lui, et je me donnerai de garde de mon iniquité.
Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
24 Et le Seigneur me rétribuera selon ma justice et selon la pureté de mes mains, présente à ses yeux.
Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
25 Avec un saint, vous serez saint, et avec un homme innocent, vous serez innocent;
Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
26 Et avec un homme excellent, vous serez excellent, et avec un pervers perversité.
ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
27 Parce que c’est vous qui sauverez un peuple humble, et qui humilierez les yeux des superbes.
Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
28 Parce que c’est vous, Seigneur, qui faites luire ma lampe; mon Dieu, illuminez mes ténèbres.
Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
29 Parce qu’avec vous je serai délivré de la tentation, et avec mon Dieu je franchirai un mur.
Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
30 Mon Dieu, sa voie est sans souillure; les paroles du Seigneur sont éprouvées par le feu; il est le protecteur de tous ceux qui espèrent en lui.
Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
31 Car qui est Dieu, excepté le Seigneur, ou qui est Dieu, excepté notre Dieu?
Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
32 Le Dieu qui m’a ceint de la force, et qui a fait ma voie sans tache.
Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
33 Qui a disposé mes pieds comme les pieds des cerfs, et m’a établi sur les lieux élevés:
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
34 Qui a instruit mes mains au combat; et vous avez rendu mes bras comme un arc d’airain.
Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
35 Et vous m’avez donné la protection de votre salut; et votre droite m’a soutenu;
Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
36 Vous avez agrandi mes pas sous moi, et mes pieds n’ont pas été affaiblis.
Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
37 Je poursuivrai mes ennemis, et je les attendrai, et je ne reviendrai point jusqu’à ce qu’ils soient entièrement défaits.
Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
38 Je les briserai, et ils ne pourront se soutenir; ils tomberont sous mes pieds.
Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
39 Et vous m’avez ceint de force pour la guerre; et ceux qui s’insurgeaient contre moi, vous les avez renversés sous moi.
Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
40 Et vous m’avez livré mes ennemis par derrière; et ceux qui me haïssaient vous les avez exterminés.
Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
41 Ils ont crié, et il n’y avait personne qui les sauvât; ils ont crié vers le Seigneur, et il ne les a pas exaucés.
Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
42 Et je les broierai comme de la poussière à la face du vent; et je les ferai disparaître comme la boue des rues.
Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
43 Vous me délivrerez des contradictions du peuple, et vous m’établirez chef de nations.
Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
44 Un peuple que je ne connaissais pas m’a servi; en écoutant de ses oreilles, il m’a obéi.
da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
45 Des fils étrangers m’ont menti, des fils étrangers ont vieilli, et ils ont chancelé en sortant de leurs voies.
Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
46 Le Seigneur vit! et béni mon Dieu! et que le Dieu de mon salut soit exalté!
Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
47 Vous, le Dieu qui me donnez des vengeances et qui me soumettez des peuples, qui me délivrez de mes ennemis furieux.
Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
48 Et vous m’élèverez au-dessus de ceux qui s’insurgent; vous m’arracherez à l’homme inique.
wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
49 À cause de cela, je vous confesserai parmi les nations, Seigneur, et je dirai un psaume à la gloire de votre nom,
Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
50 Qui exalte les victoires de son roi, et qui fait miséricorde à son christ, David, et à sa postérité pour toujours.
Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.