< Psaumes 132 >
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
2 Comme il a juré au Seigneur, et voué ce vœu au Dieu de Jacob:
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
3 Si j’entre dans l’intérieur de ma maison, si je monte sur le lit de mon repos;
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
4 Si j’accorde à mes yeux le sommeil, et à mes paupières l’assoupissement;
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
5 Et le repos à mes tempes, jusqu’à ce que je trouve un lieu pour le Seigneur, un tabernacle pour le Dieu de Jacob.
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
6 Voilà que nous avons appris qu’il était à Ephrata, nous l’avons trouvé dans les champs de la forêt.
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
7 Nous entrerons dans son tabernacle, nous adorerons dans le lieu où se sont arrêtés ses pieds,
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
8 Levez-vous, Seigneur, et entrez dans votre repos, vous et l’arche de votre sanctification.
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
9 Que vos prêtres soient revêtus de justice et que vos saints exultent.
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
10 À cause de David votre serviteur, ne détournez pas la face de votre christ.
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
11 Dieu a juré la vérité à David, et il ne l’éludera pas: Je mettrai un fils du fruit de tes entrailles sur ton trône.
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
12 Si tes fils gardent mon alliance et mes témoignages que je leur enseignerai,
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
13 Puisque le Seigneur a choisi Sion, il l’a choisi pour son habitation.
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
14 C’est là pour toujours le lieu de mon repos, j’y habiterai, puisque je l’ai choisie.
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
15 Bénissant, je bénirai sa veuve: ses pauvres, je les rassasierai de pain.
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
16 Je revêtirai ses prêtres du salut, et ses saints exulteront d’exultation.
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
17 Là je produirai la corne de David: j’ai préparé une lampe à mon christ.
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
18 Je couvrirai ses ennemis de confusion, mais sur lui fleurira ma sanctification.
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”