< Psaumes 121 >

1 J’ai levé les yeux vers les montagnes, d’où me viendra le secours.
Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
2 Mon secours vient du Seigneur, qui a fait le ciel et la terre.
Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
3 Qu’il ne permette pas que ton pied soit ébranlé, et qu’il ne s’assoupisse pas, celui qui te garde.
Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
4 Vois, il ne s’assoupira, ni ne dormira, celui qui garde Israël.
tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
5 C’est le Seigneur qui te garde, c’est le Seigneur qui est ta protection; il est sur ta main droite.
Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
6 Pendant le jour, le soleil ne le brûlera pas, ni la lune pendant la nuit.
rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
7 Le Seigneur te garde de tout mal; que le Seigneur garde ton âme.
Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
8 Que le Seigneur garde ton entrée et ta sortie, dès ce moment et jusqu’à jamais.
Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.

< Psaumes 121 >