< Psaumes 112 >

1 Bienheureux l’homme qui craint le Seigneur, il mettra toutes ses volontés dans ses commandements.
Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
2 Sa postérité sera puissante sur la terre: la génération des justes sera bénie.
’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
3 Gloire et richesses sont dans sa maison; et sa justice demeure dans les siècles des siècles.
Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
4 Il s’est élevé dans les ténèbres une lumière pour les hommes droits: le Seigneur est miséricordieux, compatissant et juste.
Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
5 Agréable est l’homme qui a de la pitié et qui prête, il réglera ses discours avec jugement;
Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
6 Parce qu’il ne sera jamais ébranlé.
Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
7 Le juste jouira d’une mémoire éternelle: il ne craindra pas d’entendre mal parler de lui. Son cœur est prêt à espérer dans le Seigneur;
Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
8 Son cœur est affermi, il ne sera pas ébranlé, jusqu’à ce qu’il méprise ses ennemis.
Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
9 Il a répandu, donné de ses biens aux pauvres: sa justice demeure dans les siècles des siècles, sa corne sera exaltée avec gloire.
Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
10 Le pécheur verra, et il sera irrité: il grincera des dents, et se consumera; le désir des pécheurs périra.
Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.

< Psaumes 112 >