< Psaumes 109 >

1 Pour la fin, psaume de David.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
2 Dieu, ne taisez pas ma louange, parce que la bouche d’un pécheur et la bouche d’un trompeur est ouverte contre moi.
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
3 Ils ont parlé contre moi avec une langue trompeuse, et de discours de haine ils m’ont environné, et ils m’ont attaqué gratuitement.
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
4 Au lieu de m’aimer, ils disaient du mal de moi; mais moi je priais.
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
5 Ils m’ont rendu des maux pour des biens, et de la haine pour mon amour.
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
6 Établissez sur lui un pécheur, et que le diable se tienne à sa droite.
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
7 Lorsqu’on le jugera, qu’il sorte condamné, et que sa prière même se tourne en péché.
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
8 Que ses jours soient réduits à un petit nombre, et qu’un autre reçoive son épiscopat.
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
9 Que ses fils deviennent orphelins, et sa femme, veuve.
Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
10 Que ses fils ballottés soient transférés d’un lieu dans un autre, et qu’ils mendient, et qu’ils soient chassés de leurs habitations.
Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
11 Qu’un usurier scrute tout ce qu’il possède, et que des étrangers ravissent le fruit de ses travaux.
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
12 Qu’il n’y ait personne qui l’assiste, et qu’il n’y ait personne qui prenne pitié de ses orphelins.
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
13 Que ses enfants soient dévoués à la mort, qu’en une seule génération son nom s’efface.
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
14 Qu’en mémoire revienne l’iniquité de ses pères, devant le Seigneur; et que le péché de sa mère ne soit point effacé.
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
15 Que ces péchés soient toujours devant le Seigneur, et que leur mémoire périsse entièrement de la terre;
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
16 Parce qu’il ne s’est point souvenu de faire miséricorde.
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
17 Et qu’il a persécuté un homme sans ressource, mendiant et brisé de douleur.
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
18 Il a aimé la malédiction, et elle viendra à lui: il n’a pas voulu la bénédiction, et elle s’éloignera de lui. Il s’est revêtu de la malédiction comme d’un vêtement, et elle est entrée comme de l’eau dans ses entrailles, et comme de l’huile dans ses os.
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
19 Qu’elle lui soit comme le vêtement dont il se couvre, et comme la ceinture dont il est toujours ceint.
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
20 Telle est, auprès du Seigneur, l’œuvre de ceux qui parlent mal de moi, de ceux qui blasphèment contre moi.
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
21 Et vous, Seigneur, Seigneur, agissez avec moi à cause de votre nom, parce que douce est votre miséricorde. Délivrez-moi,
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
22 Parce que moi, je suis indigent et pauvre, et que mon cœur s’est troublé au dedans de moi.
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
23 Comme l’ombre, lorsqu’elle déchue, j’ai été enlevé, et j’ai été chassé comme les sauterelles.
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
24 Mes genoux ont été affaiblis par le jeûne, et ma chair a été changée à cause de l’huile qui m’a manqué.
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
25 Je suis devenu un opprobre pour eux; ils m’ont vu et ils ont secoué la tête.
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
26 Aidez-moi, Seigneur mon Dieu: sauvez-moi selon votre miséricorde.
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
27 Qu’ils sachent que votre main est là, et que c’est vous, Seigneur, qui avez fait cela.
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
28 Ils me maudiront eux, et vous, vous me bénirez: que ceux qui s’insurgent contre moi soient confondus; mais votre serviteur sera dans l’allégresse.
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
29 Qu’ils soient revêtus de honte, ceux qui disent du mal de moi: qu’ils soient couverts de leur confusion comme d’un manteau.
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
30 Je glorifierai le Seigneur de toute la puissance de ma voix, je chanterai ses louanges au milieu d’une multitude.
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
31 Parce qu’il s’est tenu à la droite du pauvre, afin de sauver mon âme de ceux qui la persécutaient.
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.

< Psaumes 109 >