< Psaumes 108 >
1 Cantique de psaume, de David lui-même. Mon cœur est prêt, ô Dieu, mon cœur est prêt, je chanterai, je jouerai du psaltérion au milieu de ma gloire.
Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
2 Lève-toi, ô ma gloire, lève-toi, psaltérion, et toi, harpe: je me lèverai au point du jour.
Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
3 Je vous louerai parmi les peuples. Seigneur, et je dirai un psaume en votre honneur parmi les nations.
Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
4 Parce que votre miséricorde est grande au-dessus des cieux, et que votre vérité s’élève jusqu’aux nues.
Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
5 Soyez exalté au-dessus des cieux, ô Dieu, et que sur toute la terre éclate votre gloire,
A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
6 Afin que vos bien-aimés soient délivrés. Sauvez-moi par votre droite, et exaucez-moi;
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
7 Dieu a parlé dans son sanctuaire:
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
8 À moi est Galaad, et à moi est Manassé; Ephraïm est l’appui de ma tête.
Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
9 Moab est le vase de mon espérance.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
10 Qui me conduira dans une ville fortifiée? qui me conduira jusque dans l’Idumée?
Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
11 Ne sera-ce pas vous, ô Dieu, qui nous avez rejetés? et ne sortirez-vous point, ô Dieu, à la tête de nos armées?
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
12 Donnez-nous du secours, pour nous tirer de la tribulation, parce que vain est le salut de l’homme.
Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
13 En Dieu nous ferons preuve de valeur, et lui-même réduira au néant nos ennemis.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.